< ارمیا 6 >

ای بنی بنیامین از اورشلیم فرار کنید و کرنارا در تقوع بنوازید و علامتی بر بیت هکاریم برافرازید زیرا که بلایی از طرف شمال وشکست عظیمی رو خواهد داد. ۱ 1
“Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
و من آن دخترجمیل و لطیف یعنی دختر صهیون را منقطع خواهم ساخت. ۲ 2
Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
و شبانان با گله های خویش نزدوی خواهند آمد و خیمه های خود را گرداگرد اوبرپا نموده، هر یک در جای خود خواهند چرانید. ۳ 3
Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
با او جنگ را مهیا سازید و برخاسته، در وقت ظهر برآییم. وای بر ما زیرا که روز رو به زوال نهاده است و سایه های عصر دراز می‌شود. ۴ 4
“Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
برخیزید! و در شب برآییم تا قصرهایش رامنهدم سازیم. ۵ 5
Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
زیرا که یهوه صبایوت چنین می فرماید: «درختان را قطع نموده، مقابل اورشلیم سنگر برپا نمایید. زیرا این است شهری که سزاوار عقوبت است چونکه اندرونش تمام ظلم است. ۶ 6
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
مثل چشمه‌ای که آب خود رامی جوشاند همچنان او شرارت خویش رامی جوشاند. ظلم و تاراج در اندرونش شنیده می‌شود و بیماریها و جراحات دایم در نظر من است. ۷ 7
Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
‌ای اورشلیم، تادیب را بپذیر مبادا جان من از تو بیزار شود و تو را ویران و زمین غیرمسکون گردانم.» ۸ 8
Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
یهوه صبایوت چنین می‌گوید که «بقیه اسرائیل را مثل مو خوشه چینی خواهند کرد پس مثل کسی‌که انگور می‌چینددست خود را بر شاخه هایش برگردان.» ۹ 9
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
کیستند که به ایشان تکلم نموده، شهادت دهم تا بشنوند. هان گوش ایشان نامختون است که نتوانند شنید. اینک کلام خداوند برای ایشان عارگردیده است و در آن رغبت ندارند. ۱۰ 10
Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
و من ازحدت خشم خداوند پر شده‌ام و از خودداری خسته گردیده‌ام پس آن را در کوچه‌ها بر اطفال وبر مجلس جوانان با هم بریز. زیرا که شوهر و زن هر دو گرفتار خواهند شد و شیخ با دیرینه روز. ۱۱ 11
Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
و خانه‌ها و مزرعه‌ها و زنان ایشان با هم از آن دیگران خواهند شد زیرا خداوند می‌گوید که «دست خود را به ضد ساکنان این زمین درازخواهم کرد. ۱۲ 12
Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
چونکه جمیع ایشان چه خرد وچه بزرگ، پر از طمع شده‌اند و همگی ایشان چه نبی و چه کاهن، فریب را بعمل می‌آورند. ۱۳ 13
“Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
وجراحت قوم مرا اندک شفایی دادند، چونکه می‌گویند سلامتی است، سلامتی است با آنکه سلامتی نیست.» ۱۴ 14
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
آیا چون مرتکب رجاسات شدند خجل گردیدند؟ نی ابد خجل نشدند بلکه حیا را احساس ننمودند. بنابراین خداوندمی گوید که «در میان افتادگان خواهند افتاد وحینی که من به ایشان عقوبت رسانم خواهندلغزید.» ۱۵ 15
Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
خداوند چنین می‌گوید: «بر طریق هابایستید و ملاحظه نمایید و درباره طریق های قدیم سوآل نمایید که طریق نیکو کدام است تا درآن سلوک نموده، برای جان خود راحت بیابید، لیکن ایشان جواب دادند که در آن سلوک نخواهیم کرد. ۱۶ 16
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
و من پاسبانان بر شما گماشتم (که می‌گفتند): به آواز کرنا گوش دهید، اما ایشان گفتند گوش نخواهیم داد. ۱۷ 17
Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
پس‌ای امت هابشنوید و‌ای جماعت آنچه را که در میان ایشان است بدانید! ۱۸ 18
Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
‌ای زمین بشنو اینک من بلایی براین قوم می‌آورم که ثمره خیالات ایشان خواهدبود زیرا که به کلام من گوش ندادند و شریعت مرانیز ترک نمودند. ۱۹ 19
Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
چه فایده دارد که بخور از سباو قصب الذریره از زمین بعید برای من آورده می‌شود. قربانی های سوختنی شما مقبول نیست و ذبایح شما پسندیده من نی.» ۲۰ 20
Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
بنابراین خداوند چنین می‌گوید: «اینک من پیش روی این قوم سنگهای لغزش دهنده خواهم نهاد و پدران وپسران با هم از آنها لغزش خواهند خورد و ساکن زمین با همسایه‌اش هلاک خواهند شد.» ۲۱ 21
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
خداوند چنین می‌گوید: «اینک قومی اززمین شمال می‌آورم و امتی عظیم از اقصای زمین خواهند برخاست. ۲۲ 22
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
و کمان و نیزه خواهندگرفت. ایشان مردان ستمکیش می‌باشند که ترحم ندارند. به آواز خود مثل دریا شورش خواهندنمود و بر اسبان سوار شده، مثل مردان جنگی به ضد تو‌ای دختر صهیون صف آرایی خواهندکرد.» ۲۳ 23
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
آوازه این را شنیدیم و دستهای ما سست گردید. تنگی و درد مثل زنی که می‌زاید ما را درگرفته است. ۲۴ 24
Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
به صحرا بیرون مشوید و به راه مروید زیرا که شمشیر دشمنان و خوف از هرطرف است. ۲۵ 25
Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
‌ای دختر قوم من پلاس بپوش وخویشتن را در خاکستر بغلطان. ماتم پسر یگانه ونوحه گری تلخ برای خود بکن زیرا که تاراج کننده ناگهان بر ما می‌آید. ۲۶ 26
Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
تو را در میان قوم خودامتحان کننده و قلعه قرار دادم تا راههای ایشان رابفهمی و امتحان کنی. ۲۷ 27
“Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
همه ایشان سخت متمرد شده‌اند و برای نمامی کردن گردش می‌کنند. برنج و آهن می‌باشند و جمیع ایشان فساد کننده‌اند. ۲۸ 28
Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
دم پر زور می‌دمد و سرب درآتش فانی می‌گردد و قالگر عبث قال می‌گذاردزیرا که شریران جدا نمی شوند. ۲۹ 29
Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
نقره ترک شده نامیده می‌شوند زیرا خداوند ایشان را ترک کرده است. ۳۰ 30
Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”

< ارمیا 6 >