< ارمیا 31 >

خداوند می‌گوید: «در آن زمان من خدای تمامی قبایل اسرائیل خواهم بود و ایشان قوم من خواهند بود. ۱ 1
“A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
خداوند چنین می‌گوید: قومی که از شمشیر رستند در بیابان فیض یافتند، هنگامی که من رفتم تا برای اسرائیل آرامگاهی پیدا کنم.» ۲ 2
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
خداوند از جای دور به من ظاهر شد (وگفت ): «با محبت ازلی تو را دوست داشتم، از این جهت تو را به رحمت جذب نمودم. ۳ 3
Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
‌ای باکره اسرائیل تو را بار دیگر بنا خواهم کرد و تو بناخواهی شد و بار دیگر با دفهای خود خویشتن راخواهی آراست و در رقصهای مطربان بیرون خواهی آمد. ۴ 4
Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
بار دیگر تاکستانها بر کوههای سامره غرس خواهی نمود و غرس کنندگان غرس نموده، میوه آنها را خواهند خورد. ۵ 5
Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
زیرا روزی خواهد بود که دیده بانان بر کوهستان افرایم نداخواهند کرد که برخیزید و نزد یهوه خدای خودبه صهیون برآییم.» ۶ 6
Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
زیرا خداوند چنین می‌گوید: «به جهت یعقوب به شادمانی ترنم نمایید و به جهت سر امت‌ها آواز شادی دهید. اعلام نماییدو تسبیح بخوانید و بگویید: ای خداوند قوم خودبقیه اسرائیل را نجات بده! ۷ 7
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
اینک من ایشان را اززمین شمال خواهم آورد و از کرانه های زمین جمع خواهم نمود و با ایشان کوران و لنگان وآبستنان و زنانی که می‌زایند با هم گروه عظیمی به اینجا باز خواهند آمد. ۸ 8
Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
با گریه خواهند آمد و من ایشان را با تضرعات خواهم آورد. نزد نهرهای آب ایشان را به راه صاف که در آن نخواهند لغزیدرهبری خواهم نمود زیرا که من پدر اسرائیل هستم و افرایم نخست زاده من است. ۹ 9
Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
‌ای امت‌ها کلام خداوند را بشنوید و در میان جزایربعیده اخبار نمایید و بگویید آنکه اسرائیل راپراکنده ساخت ایشان را جمع خواهد نمود وچنانکه شبان گله خود را (نگاه دارد) ایشان رامحافظت خواهد نمود. ۱۰ 10
“Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
زیرا خداوند یعقوب را فدیه داده و او را از دست کسی‌که از او قوی تربود رهانیده است. ۱۱ 11
Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
و ایشان آمده، بر بلندی صهیون خواهند سرایید و نزد احسان خداوندیعنی نزد غله و شیره و روغن و نتاج گله و رمه روان خواهند شد و جان ایشان مثل باغ سیرآب خواهد شد و بار دیگر هرگز غمگین نخواهندگشت. ۱۲ 12
Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
آنگاه باکره‌ها به رقص شادی خواهندکرد و جوانان و پیران با یکدیگر. زیرا که من ماتم ایشان را به شادمانی مبدل خواهم کرد و ایشان را از المی که کشیده‌اند تسلی داده، فرحناک خواهم گردانید.» ۱۳ 13
’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
و خداوند می‌گوید: «جان کاهنان رااز پیه تر و تازه خواهم ساخت و قوم من از احسان من سیر خواهند شد.» ۱۴ 14
Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
خداوند چنین می‌گوید: «آوازی در رامه شنیده شد ماتم و گریه بسیار تلخ که راحیل برای فرزندان خود گریه می‌کند و برای فرزندان خود تسلی نمی پذیرد زیرا که نیستند.» ۱۵ 15
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
خداوند چنین می‌گوید: «آواز خود را ازگریه و چشمان خویش را از اشک باز دار. زیراخداوند می‌فرماید که برای اعمال خود اجرت خواهی گرفت و ایشان از زمین دشمنان مراجعت خواهند نمود. ۱۶ 16
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
و خداوند می‌گوید که به جهت عاقبت تو امید هست و فرزندانت به حدودخویش خواهند برگشت. ۱۷ 17
Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
به تحقیق افرایم راشنیدم که برای خود ماتم گرفته، می‌گفت: مراتنبیه نمودی و متنبه شدم مثل گوساله‌ای که کارآزموده نشده باشد. مرا برگردان تا برگردانیده شوم زیرا که تو یهوه خدای من هستی. ۱۸ 18
“Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
به درستی که بعد از آنکه برگردانیده شدم پشیمان گشتم و بعد از آنکه تعلیم یافتم بر ران خود زدم. خجل شدم و رسوایی هم کشیدم چونکه عارجوانی خویش را متحمل گردیدم. ۱۹ 19
Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
آیا افرایم پسر عزیز من یا ولد ابتهاج من است؟ زیرا هر گاه به ضد او سخن می‌گویم او را تا بحال به یادمی آورم. بنابراین خداوند می‌گوید که احشای من برای او به حرکت می‌آید و هر آینه بر او ترحم خواهم نمود. ۲۰ 20
Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
نشانه‌ها برای خود نصب نما وعلامت‌ها به جهت خویشتن برپا کن و دل خود رابسوی شاه راه به راهی که رفته‌ای متوجه ساز. ای باکره اسرائیل برگرد و به این شهرهای خود مراجعت نما. ۲۱ 21
“Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
‌ای دختر مرتد تا به کی به اینطرف و به آنطرف گردش خواهی نمود؟ زیراخداوند امر تازه‌ای در جهان ابداع نموده است که زن مرد را احاطه خواهد کرد.» ۲۲ 22
Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
یهوه صبایوت خدای اسرائیل چنین می‌گوید: «بار دیگر هنگامی که اسیران ایشان رابرمی گردانم، این کلام را در زمین یهودا وشهرهایش خواهند گفت که‌ای مسکن عدالت وای کوه قدوسیت، خداوند تو را مبارک سازد. ۲۳ 23
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
ویهودا و تمامی شهرهایش با هم و فلاحان و آنانی که با گله‌ها گردش می‌کنند، در آن ساکن خواهندشد. ۲۴ 24
Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
زیرا که جان خستگان را تازه ساخته‌ام وجان همه محزونان را سیر کرده‌ام.» ۲۵ 25
Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
در این حال بیدار شدم و نگریستم و خوابم برای من شیرین بود. ۲۶ 26
A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
اینک خداوند می‌گوید: «ایامی می‌آید که خاندان اسرائیل و خاندان یهودا را به بذر انسان وبذر حیوان خواهم کاشت. ۲۷ 27
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
و واقع خواهد شدچنانکه بر ایشان برای کندن و خراب نمودن ومنهدم ساختن و هلاک کردن و بلا رسانیدن مراقبت نمودم، به همینطور خداوند می‌گوید برایشان برای بنا نمودن و غرس کردن مراقب خواهم شد. ۲۸ 28
Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
و در آن ایام بار دیگر نخواهندگفت که پدران انگور ترش خوردند و دندان پسران کند گردید. ۲۹ 29
“A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
بلکه هر کس به گناه خودخواهد مرد و هر‌که انگور ترش خورد دندان وی کند خواهد شد.» ۳۰ 30
A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
خداوند می‌گوید: «اینک ایامی می‌آید که باخاندان اسرائیل و خاندان یهودا عهد تازه‌ای خواهم بست. ۳۱ 31
“Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
نه مثل آن عهدی که با پدران ایشان بستم در روزی که ایشان را دستگیری نمودم تا از زمین مصر بیرون آورم زیرا که ایشان عهد مرا شکستند، با آنکه خداوند می‌گوید من شوهر ایشان بودم.» ۳۲ 32
Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
اما خداوند می‌گوید: «اینست عهدی که بعد از این ایام با خاندان اسرائیل خواهم بست. شریعت خود را در باطن ایشان خواهم نهاد و آن را بر دل ایشان خواهم نوشت و من خدای ایشان خواهم بود و ایشان قوم من خواهند بود. ۳۳ 33
“Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
و بار دیگر کسی به همسایه‌اش و شخصی به برادرش تعلیم نخواهدداد و نخواهد گفت خداوند را بشناس. زیراخداوند می‌گوید: جمیع ایشان از خرد و بزرگ مرا خواهند شناخت، چونکه عصیان ایشان راخواهم آمرزید و گناه ایشان را دیگر به یادنخواهم آورد.» ۳۴ 34
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
خداوند که آفتاب را به جهت روشنایی روز و قانونهای ماه و ستارگان را برای روشنایی شب قرار داده است و دریا را به حرکت می‌آورد تاامواجش خروش نمایند و اسم او یهوه صبایوت می‌باشد، چنین می‌گوید. ۳۵ 35
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
پس خداوندمی گوید: «اگر این قانونها از حضور من برداشته شود، آنگاه ذریت اسرائیل نیز زایل خواهند شدتا به حضور من قوم دایمی نباشند.» ۳۶ 36
“In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
خداوندچنین می‌گوید: «اگر آسمانهای علوی پیموده شوند و اساس زمین سفلی را تفحص توان نمود، آنگاه من نیز تمامی ذریت اسرائیل را به‌سبب آنچه عمل نمودند ترک خواهم کرد. کلام خداوند این است.» ۳۷ 37
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
یهوه می‌گوید: «اینک ایامی می‌آید که این شهر از برج حننئیل تا دروازه زاویه بنا خواهدشد. ۳۸ 38
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
و ریسمان کار به خط مستقیم تا تل جارب بیرون خواهد رفت و بسوی جوعت دور خواهدزد. ۳۹ 39
Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
و تمامی وادی لاشها و خاکستر و تمامی زمینها تا وادی قدرون و بطرف مشرق تا زاویه دروازه اسبان، برای خداوند مقدس خواهد شد وبار دیگر تا ابدالاباد کنده و منهدم نخواهدگردید.» ۴۰ 40
Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”

< ارمیا 31 >