< ارمیا 22 >

خداوند چنین گفت: «به خانه پادشاه یهودا فرود آی و در آنجا به این کلام متکلم شو ۱ 1
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
و بگو: ای پادشاه یهودا که بر کرسی داود نشسته‌ای، تو و بندگانت و قومت که به این دروازه‌ها داخل می‌شوید کلام خداوند را بشنوید: ۲ 2
‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
خداوند چنین می‌گوید: انصاف وعدالت را اجرا دارید و مغصوبان را از دست ظالمان برهانید و بر غربا و یتیمان و بیوه‌زنان ستم و جور منمایید و خون بی‌گناهان را در این مکان مریزید. ۳ 3
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
زیرا اگر این کار را بجا آورید هماناپادشاهانی که بر کرسی داود بنشینند، ازدروازه های این خانه داخل خواهند شد و هر یک با بندگان و قوم خود بر ارابه‌ها و اسبان سوارخواهند گردید. ۴ 4
Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
اما اگر این سخنان را نشنویدخداوند می‌گوید که به ذات خود قسم خوردم که این خانه خراب خواهد شد. ۵ 5
Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
زیرا خداونددرباره خاندان پادشاه یهودا چنین می‌گوید: اگرچه تو نزد من جلعاد و قله لبنان می‌باشی لیکن من تو را به بیابان و شهرهای غیرمسکون مبدل خواهم ساخت. ۶ 6
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
و بر تو خراب کنندگان که هریک با آلاتش باشد معین می‌کنم و ایشان بهترین سروهای آزاد تو را قطع نموده، به آتش خواهندافکند. ۷ 7
Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
و امت های بسیار چون از این شهر عبورنمایند به یکدیگر خواهند گفت که خداوند به این شهر عظیم چرا چنین کرده است. ۸ 8
“Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
و جواب خواهند داد از این سبب که عهد یهوه خدای خودرا ترک کردند و خدایان غیر را سجده و عبادت نمودند. ۹ 9
Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
«برای مرده گریه منمایید و برای او ماتم مگیرید. زارزار بگریید برای او که می‌رود زیرا که دیگر مراجعت نخواهد کرد و زمین مولد خویش را نخواهد دید. ۱۰ 10
Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
زیرا خداوند درباره شلوم بن یوشیا پادشاه یهودا که بجای پدر خود یوشیاپادشاه شده و از این مکان بیرون رفته است چنین می گوید که دیگر به اینجا برنخواهد گشت. ۱۱ 11
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
بلکه در مکانی که او را به اسیری برده اندخواهد مرد و این زمین را باز نخواهد دید. ۱۲ 12
Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
«وای بر آن کسی‌که خانه خود را به بی‌انصافی و کوشکهای خویش را به ناحق بنامی کند که از همسایه خود مجان خدمت می‌گیردو مزدش را به او نمی دهد. ۱۳ 13
“Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
که می‌گوید خانه وسیع و اطاقهای مروح برای خود بنا می‌کنم وپنجره‌ها برای خویشتن می‌شکافد و (سقف ) آن را از سرو آزاد می‌پوشاند و با شنجرف رنگ می‌کند. ۱۴ 14
Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
آیا از این جهت که با سروهای آزادمکارمت می‌نمایی، سلطنت خواهی کرد؟ آیاپدرت اکل وشرب نمی نمود و انصاف و عدالت رابجا نمی آورد، آنگاه برایش سعادتمندی می‌بود؟ ۱۵ 15
“Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
فقیر و مسکین را دادرسی می‌نمود، آنگاه سعادتمندی می‌شد. مگر شناختن من این نیست؟ خداوند می‌گوید: ۱۶ 16
Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
اما چشمان و دل تو نیست جز برای حرص خودت و برای ریختن خون بی‌گناهان و برای ظلم و ستم تا آنها را بجا آوری. ۱۷ 17
“Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
بنابراین خداوند درباره یهویاقیم بن یوشیاپادشاه یهودا چنین می‌گوید: که برایش ماتم نخواهند گرفت و نخواهند گفت: آه‌ای برادر من یا آه‌ای خواهر و نوحه نخواهند کرد و نخواهندگفت: آه‌ای آقا یا آه‌ای جلال وی. ۱۸ 18
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
کشیده شده و بیرون از دروازه های اورشلیم بجای دورانداخته شده به دفن الاغ مدفون خواهد گردید. ۱۹ 19
Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
«به فراز لبنان برآمده، فریاد برآور و آوازخود را در باشان بلندکن. و از عباریم فریاد کن زیرا که جمیع دوستانت تلف شده‌اند. ۲۰ 20
“Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
در حین سعادتمندی تو به تو سخن گفتم، اما گفتی گوش نخواهم گرفت. همین از طفولیتت عادت تو بوده است که به آواز من گوش ندهی. ۲۱ 21
Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
باد تمامی شبانانت را خواهد چرانید و دوستانت به اسیری خواهند رفت. پس در آن وقت به‌سبب تمامی شرارتت خجل و رسوا خواهی شد. ۲۲ 22
Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
‌ای که درلبنان ساکن هستی و آشیانه خویش را درسروهای آزاد می‌سازی! هنگامی که المها و دردمثل زنی که می‌زاید تو را فرو‌گیرد چه قدر بر توافسوس خواهند کرد؟ ۲۳ 23
Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
یهوه می‌گوید: به حیات من قسم که اگر‌چه کنیاهو ابن یهویاقیم پادشاه یهودا خاتم بر دست راست من می‌بود هرآینه تو را از آنجا می‌کندم. ۲۴ 24
“Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
و تو را به‌دست آنانی که قصد جان تو دارند و به‌دست آنانی که ازایشان ترسانی و به‌دست نبوکدرصر پادشاه بابل وبه‌دست کلدانیان تسلیم خواهم نمود. ۲۵ 25
Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
و تو ومادر تو را که تو را زایید، به زمین غریبی که در آن تولد نیافتید خواهم‌انداخت که در آنجا خواهیدمرد. ۲۶ 26
Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
اما به زمینی که ایشان بسیار آرزو دارند که به آن برگردند مراجعت نخواهند نمود.» ۲۷ 27
Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
آیا این مرد کنیاهو ظرفی خوار شکسته می‌باشد و یا ظرفی ناپسندیده است؟ چرا او بااولادش به زمینی که آن را نمی شناسند انداخته وافکنده شده‌اند؟ ۲۸ 28
Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
‌ای زمین‌ای زمین‌ای زمین، کلام خداوند رابشنو! ۲۹ 29
Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
خداوند چنین می‌فرماید: «این شخص را بی‌اولاد و کسی‌که در روزگار خود کامیاب نخواهد شد بنویس، زیرا که هیچکس از ذریت وی کامیاب نخواهد شد و بر کرسی داود نخواهدنشست، و بار دیگر در یهودا سلطنت نخواهد نمود.» ۳۰ 30
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”

< ارمیا 22 >