< ارمیا 20 >

و فشحور بن امیر کاهن که ناظر اول خانه خداوند بود، ارمیا نبی را که به این امورنبوت می‌کرد شنید. ۱ 1
Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
پس فشحور ارمیای نبی رازده، او را در کنده‌ای که نزد دروازه عالی بنیامین که نزد خانه خداوند بود گذاشت. ۲ 2
sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
و در فردای آن روز فشحور ارمیا را از کنده بیرون آورد و ارمیاوی را گفت: «خداوند اسم تو را نه فشحور بلکه ماجور مسابیب خوانده است. ۳ 3
Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
زیرا خداوندچنین می‌گوید: اینک من تو را مورث ترس خودت و جمیع دوستانت می‌گردانم و ایشان به شمشیر دشمنان خود خواهند افتاد و چشمانت خواهد دید و تمامی یهودا را به‌دست پادشاه بابل تسلیم خواهم کرد که او ایشان را به بابل به اسیری برده، ایشان را به شمشیر به قتل خواهد رسانید. ۴ 4
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
و تمامی دولت این شهر و تمامی مشقت آن را وجمیع نفایس آن را تسلیم خواهم کرد و همه خزانه های پادشاهان یهودا را به‌دست دشمنان ایشان خواهم سپرد که ایشان را غارت کرده وگرفتار نموده، به بابل خواهند برد. ۵ 5
Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
و تو‌ای فشحور با جمیع سکنه خانه ات به اسیری خواهیدرفت. و تو با جمیع دوستانت که نزد ایشان به دروغ نبوت کردی، به بابل داخل شده، در آنجاخواهید مرد و در آنجا دفن خواهید شد.» ۶ 6
Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
‌ای خداوند مرا فریفتی پس فریفته شدم. ازمن زورآورتر بودی و غالب شدی. تمامی روزمضحکه شدم و هر کس مرا استهزا می‌کند. ۷ 7
Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
زیراهر گاه می‌خواهم تکلم نمایم ناله می‌کنم و به ظلم و غارت ندا می‌نمایم. زیرا کلام خداوند تمامی روز برای من موجب عار و استهزا گردیده است. ۸ 8
Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
پس گفتم که او را ذکر نخواهم نمود و بار دیگر به اسم او سخن نخواهم گفت، آنگاه در دل من مثل آتش افروخته شد و در استخوانهایم بسته گردیدو از خودداری خسته شده، باز نتوانستم ایستاد. ۹ 9
Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
زیرا که از بسیاری مذمت شنیدم و از هر جانب خوف بود و جمیع اصدقای من گفتند بر اوشکایت کنید و ما شکایت خواهیم نمود و مراقب لغزیدن من می‌باشند (و می‌گویند) که شاید اوفریفته خواهد شد تا بر وی غالب آمده، انتقام خود را از او بکشیم. ۱۰ 10
Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
لیکن خداوند با من مثل جبار قاهر است از این جهت ستمکاران من خواهند لغزید و غالب نخواهند آمد و چونکه به فطانت رفتار ننمودند به رسوایی ابدی که فراموش نخواهند شد بی‌نهایت خجل خواهندگردید. ۱۱ 11
Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
اما‌ای یهوه صبایوت که عادلان رامی آزمایی و گرده‌ها و دلها را مشاهده می‌کنی، بشود که انتقام تو را از ایشان ببینم زیرا که دعوی خویش را نزد تو کشف نمودم. ۱۲ 12
Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
برای خداوندبسرایید و خداوند را تسبیح بخوانید زیرا که جان مسکینان را از دست شریران رهایی داده است. ۱۳ 13
Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
ملعون باد روزی که در آن مولود شدم ومبارک مباد روزی که مادرم مرا زایید. ۱۴ 14
La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
ملعون باد کسی‌که پدر مرا مژده داد و گفت که برای توولد نرینه‌ای زاییده شده است و او را بسیارشادمان گردانید. ۱۵ 15
La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
و آنکس مثل شهرهایی که خداوند آنها را شفقت ننموده واژگون ساخت بشود و فریادی در صبح و نعره‌ای در وقت ظهربشنود. ۱۶ 16
Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
زیرا که مرا از رحم نکشت تا مادرم قبر من باشد و رحم او همیشه آبستن ماند. ۱۷ 17
Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
چرا ازرحم بیرون آمدم تا مشقت و غم را مشاهده نمایم و روزهایم در خجالت تلف شود؟ ۱۸ 18
Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?

< ارمیا 20 >