< اشعیا 31 >

وای بر آنانی که به جهت اعانت به مصرفرود آیند و بر اسبان تکیه نمایند و برارابه‌ها زانرو که کثیرند و بر سواران زانرو که بسیارقوی‌اند توکل کنند اما بسوی قدوس اسرائیل نظرنکنند و خداوند را طلب ننمایند. ۱ 1
Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
و او نیز حکیم است و بلا را می‌آورد و کلام خود را برنخواهدگردانید و به ضد خاندان شریران و اعانت بدکاران خواهد برخاست. ۲ 2
Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
اما مصریان انسانند و نه خداو اسبان ایشان جسدند و نه روح و خداوند دست خود را دراز می‌کند و اعانت کننده را لغزان و اعانت کرده شده را افتان گردانیده هر دوی ایشان هلاک خواهند شد. ۳ 3
Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
زیرا خداوند به من چنین گفته است چنانکه شیر و شیر ژیان بر شکار خود غرش می‌نمایدهنگامی که گروه شبانان بروی جمع شوند و ازصدای ایشان نترسیده از غوغای ایشان سر فرونمی آورد همچنان یهوه صبایوت نزول می‌فرماید تا برای کوه صهیون و تل آن مقاتله نماید. ۴ 4
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
مثل مرغان که در طیران باشند همچنان یهوه صبایوت اورشلیم را حمایت خواهد نمود وحمایت کرده، آن را رستگار خواهد ساخت و ازآن درگذشته، خلاصی خواهد داد. ۵ 5
Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
‌ای بنی‌اسرائیل بسوی آن کس که بر وی بینهایت عصیان ورزیده‌اید بازگشت نمایید. ۶ 6
Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
زیرا که در آن روز هر کدام از ایشان بتهای نقره وبتهای طلای خود را که دستهای شما آنها را به جهت گناه خویش ساخته است ترک خواهندنمود. ۷ 7
Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
آنگاه آشور به شمشیری که از انسان نباشد خواهد افتاد و تیغی که از انسان نباشد او راهلاک خواهد ساخت و او از شمشیر خواهدگریخت و جوانانش خراج گذار خواهند شد. ۸ 8
“Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
وصخره او از ترس زایل خواهد شد و سرورانش ازعلم مبهوت خواهند گردید. یهوه که آتش او درصهیون و کوره وی در اورشلیم است این رامی گوید. ۹ 9
Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.

< اشعیا 31 >