< اشعیا 20 >

در سالی که ترتان به اشدود آمد هنگامی که سرجون پادشاه آشور او رافرستاد، پس با اشدود جنگ کرده، آن را گرفت. ۱ 1
A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
در آن وقت خداوند به واسطه اشعیا ابن آموص تکلم نموده، گفت: «برو و پلاس را از کمر خودبگشا و نعلین را از پای خود بیرون کن.» و او چنین کرده، عریان و پا برهنه راه می‌رفت. ۲ 2
a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
و خداوند گفت: «چنانکه بنده من اشعیا سه سال عریان و پا برهنه راه رفته است تا آیتی وعلامتی درباره مصر و کوش باشد، ۳ 3
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
بهمان طورپادشاه آشور اسیران مصر و جلاء وطنان کوش رااز جوانان وپیران عریان و پابرهنه و مکشوف سرین خواهد برد تا رسوایی مصر باشد. ۴ 4
haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
و ایشان به‌سبب کوش که ملجای ایشان است و مصر که فخر ایشان باشد مضطرب و خجل خواهند شد. ۵ 5
Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
و ساکنان این ساحل در آن روز خواهند گفت: اینک ملجای ما که برای اعانت به آن فرار کردیم تااز دست پادشاه آشور نجات یابیم چنین شده است، پس ما چگونه نجات خواهیم یافت؟» ۶ 6
A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”

< اشعیا 20 >