< اشعیا 19 >

وحی درباره مصر: اینک خداوند بر ابر تیزرو سوار شده، به مصر می‌آید و بتهای مصر از حضور وی خواهدلرزید و دلهای مصریان در اندرون ایشان گداخته خواهد شد. ۱ 1
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
و مصریان را بر مصریان خواهم برانگیخت. برادر با برادر خود و همسایه باهمسایه خویش و شهر با شهر و کشور با کشورجنگ خواهند نمود. ۲ 2
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
و روح مصر در اندرونش افسرده شده، مشورتش را باطل خواهم گردانید وایشان از بتها و فالگیران و صاحبان اجنه وجادوگران سوال خواهند نمود. ۳ 3
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
و مصریان را به‌دست آقای ستم کیش تسلیم خواهم نمود وپادشاه زورآور بر ایشان حکمرانی خواهد کرد. خداوند یهوه صبایوت چنین می‌گوید. ۴ 4
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
و آب از دریا (نیل ) کم شده، نهر خراب وخشک خواهد گردید. ۵ 5
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
و نهرها متعفن شده، جویهای ماصور کم شده می‌خشکد و نی و بوریاپژمرده خواهد شد. ۶ 6
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
و مرغزاری که بر کنار نیل وبر دهنه نیل است و همه مزرعه های نیل خشک ورانده شده و نابود خواهد گردید. ۷ 7
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
و ماهی گیران ماتم می‌گیرند و همه آنانی که قلاب به نیل اندازندزاری می‌کنند و آنانی که دام بر روی آب گسترانند افسرده خواهند شد. ۸ 8
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
و عاملان کتان شانه زده و بافندگان پارچه سفید خجل خواهندشد. ۹ 9
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
و ارکان او ساییده و جمیع مزدوران رنجیده دل خواهند شد. ۱۰ 10
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
سروران صوعن بالکل احمق می‌شوند ومشورت مشیران دانشمند فرعون وحشی می گردد. پس چگونه به فرعون می‌گویید که من پسر حکما و پسر پادشاهان قدیم می‌باشم. ۱۱ 11
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
پس حکیمان تو کجایند تا ایشان تو را اطلاع دهند وبدانند که یهوه صبایوت درباره مصر چه تقدیرنموده است. ۱۲ 12
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
سروران صوعن ابله شده وسروران نوف فریب خورده‌اند و آنانی که سنگ زاویه اسباط مصر هستند آن را گمراه کرده‌اند. ۱۳ 13
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
و خداوند روح خیرگی در وسط آن آمیخته است که ایشان مصریان را در همه کارهای ایشان گمراه کرده‌اند مثل مستان که در قی خود افتان وخیزان راه می‌روند. ۱۴ 14
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
و مصریان را کاری نخواهد ماند که سر یا دم نخل یا بوریا بکند. ۱۵ 15
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
در آن روز اهل مصر مثل زنان می‌باشند و ازحرکت دست یهوه صبایوت که آن را بر مصر به حرکت می‌آورد لرزان و هراسان خواهند شد. ۱۶ 16
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
و زمین یهودا باعث خوف مصر خواهد شد که هرکه ذکر آن را بشنود خواهد ترسید به‌سبب تقدیری که یهوه صبایوت بر آن مقدر نموده است. ۱۷ 17
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
در آن روز پنج شهر در زمین مصر به زبان کنعان متکلم شده، برای یهوه صبایوت قسم خواهند خورد و یکی شهر هلاکت نامیده خواهدشد. ۱۸ 18
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
در آن روز مذبحی برای خداوند در میان زمین مصر و ستونی نزد حدودش برای خداوندخواهد بود. ۱۹ 19
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
و آن آیتی و شهادتی برای یهوه صبایوت در زمین مصر خواهد بود. زیرا که نزدخداوند به‌سبب جفاکنندگان خویش استغاثه خواهد نمود و او نجات‌دهنده و حمایت کننده‌ای برای ایشان خواهد فرستاد و ایشان راخواهد رهانید. ۲۰ 20
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
و خداوند بر مصریان معروف خواهد شد و در آن روز مصریان خداوند راخواهند شناخت و با ذبایح و هدایا او را عبادت خواهند کرد و برای خداوند نذر کرده، آن را وفاخواهند نمود. ۲۱ 21
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
و خداوند مصریان را خواهدزد و به زدن شفا خواهد داد زیرا چون بسوی خداوند بازگشت نمایند ایشان را اجابت نموده، شفا خواهد داد. ۲۲ 22
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
در آن روز شاهراهی از مصر به آشورخواهد بود و آشوریان به مصر و مصریان به آشورخواهند رفت و مصریان با آشوریان عبادت خواهند نمود. ۲۳ 23
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
در آن روز اسرائیل سوم مصر وآشور خواهد شد و آنها در میان جهان برکت خواهند بود. ۲۴ 24
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
زیرا که یهوه صبایوت آنها رابرکت داده خواهد گفت قوم من مصر و صنعت دست من آشور و میراث من اسرائیل مبارک باشند. ۲۵ 25
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”

< اشعیا 19 >