< حَجّای 2 >

در روز بیست و یکم ماه هفتم، کلام خداوند بواسطه حجی نبی نازل شده، گفت: ۱ 1
a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
زربابل بن شالتیئیل والی یهودا و یهوشع بن یهوصادق رئیس کهنه، و بقیه قوم را خطاب کرده، بگو: ۲ 2
“Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
کیست در میان شما که باقی‌مانده واین خانه را در جلال نخستینش دیده باشد؟ پس الان در نظر شما چگونه می‌نماید؟ آیا در نظر شماناچیز نمی نماید؟ ۳ 3
‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
اما الان خداوند می‌گوید: ای زربابل قوی‌دل باش و‌ای یهوشع بن یهوصادق رئیس کهنه قوی‌دل باش و‌ای تمامی قوم زمین قوی‌دل باشید و خداوند می‌فرماید که مشغول بشوید زیرا که من با شما هستم. قول یهوه صبایوت این است. ۴ 4
Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
برحسب کلام آن عهدی که در حین بیرون آوردن شما از مصر با شما بستم وچونکه روح من در میان شما قایم می‌باشد، ترسان مباشید. ۵ 5
‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
زیرا که یهوه صبایوت چنین می‌گوید: یک دفعه دیگر و آن نیز بعد از اندک زمانی، آسمانها و زمین و دریا و خشکی را متزلزل خواهم ساخت. ۶ 6
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
و تمامی امت‌ها را متزلزل خواهم ساخت و فضیلت جمیع امت‌ها خواهندآمد و یهوه صبایوت می‌گوید که این خانه را ازجلال پر خواهم ساخت. ۷ 7
Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
یهوه صبایوت می‌گوید: نقره از آن من و طلا از آن من است. ۸ 8
‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
یهوه صبایوت می‌گوید: جلال آخر این خانه ازجلال نخستینش عظیم تر خواهد بود و در این مکان، سلامتی را خواهم بخشید. قول یهوه صبایوت این است. ۹ 9
‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
در روز بیست و چهارم ماه نهم از سال دوم داریوش، کلام خداوند بواسطه حجی نبی نازل شده، گفت: ۱۰ 10
A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
یهوه صبایوت چنین می‌گوید: ازکاهنان درباره شریعت سوال کن و بپرس. ۱۱ 11
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
اگرکسی گوشت مقدس را در دامن جامه خود برداردو دامنش به نان یا آش یا شراب یا روغن یا به هرقسم خوراک دیگر برخورد، آیا آن مقدس خواهد شد؟ و کاهنان جواب دادند که نی. ۱۲ 12
Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
پس حجی پرسید: اگر کسی‌که از میتی نجس شده باشد یکی از اینها را لمس نماید آیا آن نجس خواهد شد؟ و کاهنان در جواب گفتند که نجس خواهد شد. ۱۳ 13
Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
پس حجی تکلم نموده، گفت: خداوند می‌فرماید این قوم همچنین هستند و این امت به نظر من همچنین می‌باشند و همه اعمال دستهای ایشان چنین است و هر هدیه‌ای که درآنجا می‌برند نجس می‌باشد. ۱۴ 14
Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
و الان دل خود رامشغول سازید از این‌روز و قبل از این، پیش ازآنکه سنگی برسنگی در هیکل خداوند گذاشته شود. ۱۵ 15
“‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
در تمامی این ایام چون کسی به توده بیست (من ) می‌آمد فقط ده (من ) بود و چون کسی به میخانه می‌آمد تا پنجاه رطل از آن بکشد، فقطبیست رطل بود. ۱۶ 16
A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
و شما را و تمامی اعمال دستهای شما را به باد سموم و یرقان و تگرگ زدم. لیکن خداوند می‌گوید بسوی من بازگشت ننمودید. ۱۷ 17
Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
الان دل خود را مشغول سازید از این‌روز به بعد، یعنی از روز بیست و چهارم ماه نهم، از روزی که بنیاد هیکل خداوند نهاده شد، دل خود را مشغول سازید. ۱۸ 18
‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
آیا تخم هنوز در انباراست و مو و انجیر و انار و درخت زیتون هنوزمیوه خود را نیاورده‌اند؟ از این‌روز برکت خواهم داد. ۱۹ 19
Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
و کلام خداوند بار دوم در بیست و چهارم ماه بر حجی نازل شده، گفت: ۲۰ 20
Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
زربابل والی یهودا را خطاب کرده، بگو: من آسمانها و زمین رامتزلزل خواهم ساخت. ۲۱ 21
“Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
و کرسی ممالک را واژگون خواهم نمود و قوت ممالک امت‌ها راهلاک خواهم ساخت و ارابه‌ها و سواران آنها راسرنگون خواهم کرد و اسبها و سواران آنها به شمشیر یکدیگر خواهند افتاد. ۲۲ 22
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
یهوه صبایوت می گوید: در آن روز‌ای بنده من زربابل بن شالتیئیل، تو را خواهم گرفت و خداوند می‌گویدکه تو را مثل نگین خاتم خواهم ساخت زیرا که من تو را برگزیده‌ام. قول یهوه صبایوت این است. می گوید: در آن روز‌ای بنده من زربابل بن شالتیئیل، تو را خواهم گرفت و خداوند می‌گویدکه تو را مثل نگین خاتم خواهم ساخت زیرا که من تو را برگزیده‌ام. قول یهوه صبایوت این است. ۲۳ 23
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< حَجّای 2 >