< حبقوق 2 >

بر دیده بانگاه خود می‌ایستم و بر برج برپامی شوم. و مراقب خواهم شد تا ببینم که اوبه من چه خواهد گفت و درباره شکایتم چه جواب خواهد داد. ۱ 1
Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
پس خداوند مرا جواب دادو گفت: رویا را بنویس و آن را بر لوحها چنان نقش نما که دونده آن را بتواند خواند. ۲ 2
Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
زیرا که رویا هنوز برای وقت معین است و به مقصدمی شتابد و دروغ نمی گوید. اگر‌چه تاخیر نمایدبرایش منتظر باش زیرا که البته خواهد آمد ودرنگ نخواهد نمود. ۳ 3
Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
اینک جان مرد متکبر در اوراست نمی باشد، اما مرد عادل به ایمان خودزیست خواهد نمود. ۴ 4
“Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
به درستی که شراب فریبنده است و مرد مغرور آرامی نمی پذیرد، که شهوت خود را مثل عالم اموات می‌افزاید وخودش مثل موت، سیر نمی شود. بلکه جمیع امت‌ها را نزد خود جمع می‌کند و تمامی قوم‌ها رابرای خویشتن فراهم می‌آورد. (Sheol h7585) ۵ 5
ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol h7585)
پس آیا جمیع ایشان بر وی مثلی نخواهند زد و معمای طعن آمیز بر وی (نخواهند‌آورد)؟ و نخواهندگفت: وای بر کسی‌که آنچه را که از آن وی نیست می‌افزاید؟ تا به کی؟ و خویشتن را زیر بار رهنهامی نهد. ۶ 6
“Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
آیا گزندگان بر تو ناگهان برنخواهندخاست و آزارندگانت بیدار نخواهند شد و تو راتاراج نخواهند نمود؟ ۷ 7
Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
چونکه تو امت های بسیاری را غارت کرده‌ای، تمامی بقیه قوم‌ها تو راغارت خواهند نمود، به‌سبب خون مردمان وظلمی که بر زمین و شهر و جمیع ساکنانش نموده‌ای. ۸ 8
Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
وای بر کسی‌که برای خانه خود بدی راکسب نموده است تا آشیانه خود را بر جای بلندساخته، خویشتن را از دست بلا برهاند. ۹ 9
“Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
رسوایی را به جهت خانه خویش تدبیرکرده‌ای به اینکه قوم های بسیار را قطع نموده و برضد جان خویش گناه ورزیده‌ای. ۱۰ 10
Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
زیراکه سنگ از دیوار فریاد برخواهد آورد و تیر از میان چوبها آن را جواب خواهد داد. ۱۱ 11
Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
وای بر کسی‌که شهری به خون بنا می‌کند و قریه‌ای به بی‌انصافی استوار می‌نماید. ۱۲ 12
“Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
آیا این از جانب یهوه صبایوت نیست که قوم‌ها برای آتش مشقت می‌کشند و طوایف برای بطالت خویشتن راخسته می‌نمایند؟ ۱۳ 13
Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
زیرا که جهان از معرفت جلال خداوند مملو خواهد شد به نحوی که آبهادریا را مستور می‌سازد. ۱۴ 14
Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
وای بر کسی‌که همسایه خود را می‌نوشاندو بر تو که زهر خویش را ریخته، او را نیز مست می‌سازی تا برهنگی او را بنگری. ۱۵ 15
“Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
تو ازرسوایی به عوض جلال سیر خواهی شد. تو نیزبنوش و غلفه خویش را منکشف ساز. کاسه دست راست خداوند بر تو وارد خواهد آمد و قی رسوایی بر جلال تو خواهد بود. ۱۶ 16
Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
زیرا ظلمی که بر لبنان نمودی و هلاکت حیوانات که آنها راترسانیده بود، تو را خواهد پوشانید. به‌سبب خون مردمان و ظلمی که بر زمین و شهر و بر جمیع ساکنانش رسانیدی. ۱۷ 17
Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
از بت تراشیده چه فایده است که سازنده آن، آن را بتراشد یا از بت ریخته شده و معلم دروغ، که سازنده آن بر صنعت خودتوکل بنماید و بتهای گنگ را بسازد. ۱۸ 18
“Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
وای برکسی‌که به چوب بگوید بیدار شو و به سنگ گنگ که برخیز! آیا می‌شود که آن تعلیم دهد؟ اینک به طلا و نقره پوشیده می‌شود لکن در اندرونش مطلق روح نیست. ۱۹ 19
Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
اما خداوند در هیکل قدس خویش است پس تمامی جهان به حضور وی خاموش باشد. ۲۰ 20
Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.

< حبقوق 2 >