< پیدایش 15 >

بعد از این وقایع، کلام خداوند دررویا، به ابرام رسیده، گفت: «ای ابرام مترس، من سپر تو هستم، و اجر بسیار عظیم تو.» ۱ 1
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
ابرام گفت: «ای خداوند یهوه، مرا چه خواهی داد، و من بی‌اولاد می‌روم، و مختارخانه‌ام، این العاذار دمشقی است؟» ۲ 2
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
و ابرام گفت: «اینک مرا نسلی ندادی، و خانه زادم وارث من است.» ۳ 3
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
در ساعت، کلام خداوند به وی دررسیده، گفت: «این وارث تو نخواهد بود، بلکه کسی‌که از صلب تو درآید، وارث تو خواهدبود.» ۴ 4
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
و او را بیرون آورده، گفت: «اکنون بسوی آسمان بنگر و ستارگان را بشمار، هرگاه آنها راتوانی شمرد.» پس به وی گفت: «ذریت تو چنین خواهد بود.» ۵ 5
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
و به خداوند ایمان آورد، و او، این را برای وی عدالت محسوب کرد. ۶ 6
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
پس وی راگفت: «من هستم یهوه که تو را از اور کلدانیان بیرون آوردم، تا این زمین را به ارثیت، به تو بخشم.» ۷ 7
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
گفت: «ای خداوند یهوه، به چه نشان بدانم که وارث آن خواهم بود؟» ۸ 8
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
به وی گفت: «گوساله ماده سه ساله و بز ماده سه ساله و قوچی سه ساله و قمری و کبوتری برای من بگیر.» ۹ 9
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
پس این همه را بگرفت، و آنها را از میان، دوپاره کرد، و هر پاره‌ای را مقابل جفتش گذاشت، لکن مرغان را پاره نکرد. ۱۰ 10
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
و چون لاشخورها برلاشه‌ها فرود آمدند، ابرام آنها را راند. ۱۱ 11
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
و چون آفتاب غروب می‌کرد، خوابی گران بر ابرام مستولی شد، و اینک تاریکی ترسناک سخت، اورا فرو گرفت. ۱۲ 12
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
پس به ابرام گفت: «یقین بدان که ذریت تو در زمینی که از آن ایشان نباشد، غریب خواهند بود، و آنها را بندگی خواهند کرد، و آنهاچهارصد سال ایشان را مظلوم خواهند داشت. ۱۳ 13
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
و بر آن امتی که ایشان بندگان آنها خواهند بود، من داوری خواهم کرد. و بعد از آن با اموال بسیاربیرون خواهند آمد. ۱۴ 14
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
و تو نزد پدران خود به سلامتی خواهی رفت، و در‌پیری نیکو مدفون خواهی شد. ۱۵ 15
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
و در پشت چهارم بدینجاخواهند برگشت، زیرا گناه اموریان هنوز تمام نشده است.» ۱۶ 16
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
و واقع شد که چون آفتاب غروب کرده بودو تاریک شد، تنوری پر دود و چراغی مشتعل ازمیان آن پاره‌ها گذر نمود. ۱۷ 17
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
در آن روز، خداوندبا ابرام عهد بست و گفت: «این زمین را از نهر مصرتا به نهر عظیم، یعنی نهر فرات، به نسل توبخشیده‌ام، ۱۸ 18
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
یعنی قینیان و قنزیان و قدمونیان وحتیان و فرزیان و رفائیان، ۱۹ 19
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
و اموریان و کنعانیان و جرجاشیان و یبوسیان را.» ۲۰ 20
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
۲۱ 21
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”

< پیدایش 15 >