< پیدایش 13 >

و ابرام با زن خود، و تمام اموال خویش، و لوط، از مصر به جنوب آمدند. ۱ 1
Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
وابرام از مواشی و نقره و طلا، بسیار دولتمند بود. ۲ 2
Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
پس، از جنوب، طی منازل کرده، به بیت ئیل آمد، بدانجایی که خیمه‌اش در ابتدا بود، در میان بیت ئیل و عای، ۳ 3
Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
به مقام آن مذبحی که اول بنانهاده بود، و در آنجا ابرام نام یهوه را خواند. ۴ 4
da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
ولوط را نیز که همراه ابرام بود، گله و رمه و خیمه هابود. ۵ 5
Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
و زمین گنجایش ایشان را نداشت که دریکجا ساکن شوند زیرا که اندوخته های ایشان بسیار بود، و نتوانستند در یک جا سکونت کنند. ۶ 6
Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
و در میان شبانان مواشی ابرام و شبانان مواشی لوط نزاع افتاد. و در آن هنگام کنعانیان و فرزیان، ساکن زمین بودند. ۷ 7
Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
پس ابرام به لوط گفت: «زنهاردر میان من و تو، و در میان شبانان من و شبانان تونزاعی نباشد، زیرا که ما برادریم. ۸ 8
Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
مگر تمام زمین پیش روی تو نیست؟ ملتمس اینکه از من جداشوی. اگر به‌جانب چپ روی، من بسوی راست خواهم رفت و اگر بطرف راست روی، من به‌جانب چپ خواهم رفت.» ۹ 9
Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
آنگاه لوط چشمان خود را برافراشت، وتمام وادی اردن را بدید که همه‌اش مانند باغ خداوند و زمین مصر، به طرف صوغر، سیراب بود، قبل از آنکه خداوند سدوم و عموره راخراب سازد. ۱۰ 10
Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
پس لوط تمام وادی اردن را برای خود اختیار کرد، و لوط بطرف شرقی کوچ کرد، واز یکدیگر جدا شدند. ۱۱ 11
Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
ابرام در زمین کنعان ماند، و لوط در بلاد وادی ساکن شد، و خیمه خودرا تا سدوم نقل کرد. ۱۲ 12
Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
لکن مردمان سدوم بسیار شریر و به خداوند خطاکار بودند. ۱۳ 13
Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
و بعد از جداشدن لوط از وی، خداوند به ابرام گفت: «اکنون توچشمان خود را برافراز و از مکانی که در آن هستی، بسوی شمال و جنوب، و مشرق و مغرب بنگر ۱۴ 14
Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
زیرا تمام این زمین را که می‌بینی به تو وذریت تو تا به ابد خواهم بخشید. ۱۵ 15
Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
و ذریت تو رامانند غبار زمین گردانم. چنانکه اگر کسی غبارزمین را تواند شمرد، ذریت تو نیز شمرده شود. ۱۶ 16
Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
برخیز و در طول و عرض زمین گردش کن زیراکه آن را به تو خواهم داد.» ۱۷ 17
Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
و ابرام خیمه خودرا نقل کرده، روانه شد و در بلوطستان ممری که در حبرون است، ساکن گردید، و در آنجا مذبحی برای یهوه بنا نهاد. ۱۸ 18
Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.

< پیدایش 13 >