< حزقیال 30 >

و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت: ۱ 1
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان نبوت کرده، بگو: خداوند یهوه چنین می‌فرماید: ولوله کنید وبگویید وای برآن روز! ۲ 2
“Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
زیرا که آن روز نزدیک است و روز خداوند نزدیک است! روز ابرها وزمان امت‌ها خواهد بود! ۳ 3
Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
و شمشیری بر مصرفرود می‌آید. و چون کشتگان در مصر بیفتند، آنگاه درد شدیدی بر حبش مستولی خواهد شد. و جمعیت آن را گرفتار خواهد کرد و اساسهایش منهدم خواهد گردید. ۴ 4
Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
و حبش و فوط ولود وتمامی قومهای مختلف و کوب و اهل زمین عهدهمراه ایشان به شمشیر خواهند افتاد.» ۵ 5
Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
وخداوند چنین می‌فرماید: «معاونان مصر خواهندافتاد و فخر قوت آن فرود خواهد آمد. و ازمجدل تا اسوان در میان آن به شمشیر خواهندافتاد. قول خداوند یهوه این است. ۶ 6
“‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و در میان زمینهای ویران ویران خواهند شد و شهرهایش در میان و شهرهای مخروب خواهد بود. ۷ 7
Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
وچون آتشی در مصر افروخته باشم و جمیع انصارش شکسته شوند، آنگاه خواهند دانست که من یهوه هستم. ۸ 8
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
در آن روز قاصدان از حضور من به کشتیها بیرون رفته، حبشیان مطمئن را خواهندترسانید. و بر ایشان درد شدیدی مثل روز مصرمستولی خواهد شد، زیرا اینک آن می‌آید.» ۹ 9
“‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
وخداوند یهوه چنین می‌گوید: «من جمعیت مصررا به‌دست نبوکدرصر پادشاه بابل تباه خواهم ساخت. ۱۰ 10
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
او با قوم خود و ستمکیشان امت هاآورده خواهند شد تا آن زمین ویران را سازند. وشمشیرهای خود را بر مصر کشیده، زمین را از کشتگان پر خواهند ساخت. ۱۱ 11
Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
و نهرها را خشک گردانیده، زمین را به‌دست اشرار خواهم فروخت. و زمین را با هرچه در آن است، به‌دست غریبان ویران خواهم ساخت. من که یهوه هستم گفته‌ام.» ۱۲ 12
Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
و خداوند یهوه چنین می‌فرماید: «بتها رانابود ساخته، اصنام را از نوف تلف خواهم نمود. و بار دیگر رئیسی از زمین مصر نخواهدبرخاست. و خوف بر زمین مصر مستولی خواهم ساخت. ۱۳ 13
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
و فترس را خراب نموده، آتشی درصوعن خواهم افروخت. و بر نو داوری خواهم نمود. ۱۴ 14
Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
و غضب خود را برسین که ملاذ مصراست ریخته، جمعیت نو را منقطع خواهم ساخت. ۱۵ 15
Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
و چون آتشی در مصر افروخته باشم، سین به درد سخت مبتلا و نومفتوح خواهد شد. وخصمان در وقت روز بر نوف خواهند آمد. ۱۶ 16
Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
جوانان آون و فیبست به شمشیر خواهند افتادو اهل آنها به اسیری خواهند رفت. ۱۷ 17
Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
و روزدرتحفنحیس تاریک خواهد شد حینی که یوغهای مصر را در آنجا شکسته باشم و فخرقوتش در آن تلف شده باشد. و ابرها آن را خواهدپوشانید و دخترانش به اسیری خواهند رفت. ۱۸ 18
Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
پس چون بر مصر داوری کرده باشم، آنگاه خواهند دانست که من یهوه هستم.» ۱۹ 19
Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
و در روز هفتم ماه اول از سال یازدهم، کلام خداوند بر من نازل شده، گفت: ۲۰ 20
A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان بازوی فرعون پادشاه مصر را خواهم شکست. واینک شکسته بندی نخواهد شد و بر آن مرهم نخواهند گذارد و کرباس نخواهند بست تا قادر برگرفتن شمشیر بشود. ۲۱ 21
“Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
بنابراین خداوند یهوه چنین می‌گوید: هان من به ضد فرعون پادشاه مصرهستم و هر دو بازوی او هم درست و هم شکسته را خرد خواهم کرد و شمشیر را از دستش خواهم انداخت. ۲۲ 22
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
و مصریان را در میان امت‌ها پراکنده و در میان کشورها متفرق خواهم ساخت. ۲۳ 23
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
وبازوهای پادشاه بابل را تقویت نموده، شمشیرخود را به‌دست او خواهم داد. و بازوهای فرعون را خواهم شکست که به حضور وی به ناله کشتگان ناله خواهد کرد. ۲۴ 24
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
پس بازوهای پادشاه بابل را تقویت خواهم نمود. و بازوهای فرعون خواهد افتاد و چون شمشیر خود را به‌دست پادشاه بابل داده باشم و او آن را بر زمین مصر درازکرده باشد، آنگاه خواهند دانست که من یهوه هستم. ۲۵ 25
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
و چون مصریان را در میان امت هاپراکنده و ایشان را در کشورها متفرق ساخته باشم، ایشان خواهند دانست که من یهوه هستم.» ۲۶ 26
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< حزقیال 30 >