< حزقیال 16 >

و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت: ۱ 1
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان اورشلیم را ازرجاساتش آگاه ساز! ۲ 2
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
و بگو خداوند یهوه به اورشلیم چنین می‌فرماید: اصل و ولادت تو اززمین کنعان است. پدرت اموری و مادرت حتی بود. ۳ 3
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
و اما ولادت تو. در روزی که متولد شدی نافت را نبریدند و تو را به آب غسل ندادند و طاهرنساختند و نمک نمالیدند و به قنداقه نپیچیدند. ۴ 4
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
چشمی بر تو شفقت ننمود و بر تو مرحمت نفرمود تا یکی از اینکارها را برای تو بعمل آورد. بلکه در روز ولادتت جان تو را خوار شمرده، تورا بر روی صحرا انداختند. ۵ 5
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
و من از نزد تو گذرنمودم و تو را در خونت غلطان دیدم. پس تو راگفتم: ای که به خونت آلوده هستی زنده شو! بلی گفتم: ای که به خونت آلوده هستی، زنده شو! ۶ 6
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
وتو را مثل نباتات صحرا بسیار افزودم تا نمو کرده، بزرگ شدی و به زیبایی کامل رسیدی. پستانهایت برخاسته و مویهایت بلند شد، لیکن برهنه و عریان بودی. ۷ 7
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
«و چون از تو گذر کردم برتو نگریستم واینک زمان تو زمان محبت بود. پس دامن خود رابر تو پهن کرده، عریانی تو را مستور ساختم و خداوند یهوه می‌گوید که با تو قسم خوردم و با توعهد بستم و از آن من شدی. ۸ 8
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و تو را به آب غسل داده، تو را از خونت طاهر ساختم و تو را به روغن تدهین کردم. ۹ 9
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
و تو را به لباس قلابدوزی ملبس ساختم و نعلین پوست خز به پایت کردم و تو را به کتان نازک آراسته و به ابریشم پیراسته ساختم. ۱۰ 10
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
و تو را به زیورها زینت داده، دستبندها بردستت و گردن بندی بر گردنت نهادم. ۱۱ 11
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
وحلقه‌ای در بینی و گوشواره‌ها در گوشهایت و تاج جمالی بر سرت نهادم. ۱۲ 12
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
پس با طلا و نقره آرایش یافتی و لباست از کتان نازک و ابریشم قلابدوزی بود و آرد میده و عسل و روغن خوردی و بی‌نهایت جمیل شده، به درجه ملوکانه ممتاز گشتی. ۱۳ 13
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
و آوازه تو به‌سبب زیباییت درمیان امت‌ها شایع شد. زیرا خداوند یهوه می‌گویدکه آن زیبایی از جمال من که بر تو نهاده بودم کامل شد. ۱۴ 14
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
«اما بر زیبایی خود توکل نمودی و به‌سبب آوازه خویش زناکار گردیدی و زنای خویش را برهر رهگذری ریختی و از آن او شد. ۱۵ 15
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
و ازلباسهای خود گرفتی و مکان های بلند رنگارنگ برای خود ساخته، بر آنها زنا نمودی که مثل اینکارها واقع نشده و نخواهد شد. ۱۶ 16
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
و زیورهای زینت خود را از طلا و نقره (من که به تو داده بودم )گرفته، تمثالهای مردان را ساخته با آنها زنانمودی. ۱۷ 17
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
و لباس قلابدوزی خود را گرفته، به آنها پوشانیدی و روغن و بخور مرا پیش آنهاگذاشتی. ۱۸ 18
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
و نان مرا که به تو داده بودم و آردمیده و روغن و عسل را که رزق تو ساخته بودم، پیش آنها برای هدیه خوشبویی نهادی و چنین شد. قول خداوند یهوه این است. ۱۹ 19
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و پسران ودخترانت را که برای من زاییده بودی گرفته، ایشان را به جهت خوراک آنها ذبح نمودی. آیا زنا کاری تو کم بود ۲۰ 20
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
که پسران مرا نیز کشتی و ایشان راتسلیم نمودی که برای آنها از آتش گذرانیده شوند؟ ۲۱ 21
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
و در تمامی رجاسات و زنای خود ایام جوانی خود را حینی که عریان و برهنه بودی و درخون خود می‌غلطیدی بیاد نیاوردی.» ۲۲ 22
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
و خداوند یهوه می‌گوید: «وای بر تو! وای بر تو! زیرا بعد از تمامی شرارت خود، ۲۳ 23
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
خراباتها برای خود بنا نمودی و عمارات بلنددر هر کوچه برای خود ساختی. ۲۴ 24
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
بسر هر راه عمارتهای بلند خود را بنا نموده، زیبایی خود رامکروه ساختی و برای هر راهگذری پایهای خویش را گشوده، زناکاریهای خود را افزودی. ۲۵ 25
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
و با همسایگان خود پسران مصر که بزرگ گوشت می‌باشند، زنا نمودی و زناکاری خود راافزوده، خشم مرا بهیجان آوردی. ۲۶ 26
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
لهذا اینک من دست خود را بر تو دراز کرده، وظیفه تو را قطع نمودم و تو را به آرزوی دشمنانت یعنی دختران فلسطینیان که از رفتار قبیح تو خجل بودند، تسلیم نمودم. ۲۷ 27
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
و چونکه سیر نشدی با بنی آشور نیز زنا نمودی و با ایشان نیز زنا نموده، سیرنگشتی. ۲۸ 28
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
و زناکاریهای خود را از زمین کنعان تازمین کلدانیان زیاد نمودی و از این هم سیرنشدی.» ۲۹ 29
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
خداوند یهوه می‌گوید: «دل تو چه قدرضعیف است که تمامی این اعمال را که کار زن زانیه سلیطه می‌باشد، بعمل آوردی. ۳۰ 30
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
که بسرهر راه خرابات خود را بنا نمودی و در هر کوچه عمارات بلند خود را ساختی و مثل فاحشه های دیگر نبودی چونکه اجرت را خوار شمردی. ۳۱ 31
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
‌ای زن زانیه که غریبان را به‌جای شوهر خودمی گیری! ۳۲ 32
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
به جمیع فاحشه‌ها اجرت می‌دهند. ۳۳ 33
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
و عادت تو درزناکاریت برعکس سایر زنان است. چونکه کسی به جهت زناکاری از عقب تو نمی آید و تو اجرت می‌دهی و کسی به تو اجرت نمی دهد. پس عادت تو بر عکس دیگران است.» ۳۴ 34
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
بنابراین‌ای زانیه! کلام خداوند را بشنو! ۳۵ 35
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
خداوند یهوه چنین می‌گوید: «چونکه نقد توریخته شد و عریانی تو از زناکاریت با عاشقانت وبا همه بتهای رجاساتت و از خون پسرانت که به آنها دادی مکشوف گردید، ۳۶ 36
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
لهذا هان من جمیع عاشقانت را که به ایشان ملتذ بودی و همه آنانی راکه دوست داشتی، با همه کسانی که از ایشان نفرت داشتی جمع خواهم نمود. و ایشان را از هرطرف نزد تو فراهم آورده، برهنگی تو را به ایشان مکشوف خواهم ساخت، تا تمامی عریانیت راببینند. ۳۷ 37
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
و بر تو فتوای زنانی را که زنا می‌کنند وخونریز می‌باشند، خواهم داد. و خون غضب وغیرت را بر تو وارد خواهم آورد. ۳۸ 38
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
و تو را به‌دست ایشان تسلیم نموده، خراباتهای تو راخراب و عمارات بلند تو را منهدم خواهندساخت. و لباست را از تو خواهند کند و زیورهای قشنگ تو را خواهند گرفت و تو را عریان و برهنه خواهند گذاشت. ۳۹ 39
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
و گروهی بر تو آورده، تو رابه سنگها سنگسار خواهند کرد و به شمشیرهای خود تو را پاره پاره خواهند نمود. ۴۰ 40
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
و خانه های تو را به آتش سوزانیده، در نظر زنان بسیار بر توعقوبت خواهند رسانید. پس من تو را از زنا کاری بازخواهم داشت و بار دیگر اجرت نخواهی داد. ۴۱ 41
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
و حدت خشم خود را بر تو فرو خواهم نشانیدو غیرت من از تو خواهد برگشت و آرام گرفته، بار دیگر غضب نخواهم نمود. ۴۲ 42
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
چونکه ایام جوانی خود را به یاد نیاورده، مرا به همه اینکارهارنجانیدی، از این جهت خداوند یهوه می‌گوید که اینک نیز رفتار تو را بر سرت وارد خواهم آورد وعلاوه بر تمامی رجاساتت دیگر این عمل قبیح رامرتکب نخواهی شد. ۴۳ 43
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
«اینک هر‌که مثل می‌آورد این مثل را بر توآورده، خواهد گفت که مثل مادر، مثل دخترش می‌باشد. ۴۴ 44
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
تو دختر مادر خود هستی که ازشوهر و پسران خود نفرت می‌داشت. و خواهرخواهران خود هستی که از شوهران و پسران خویش نفرت می‌دارند. مادر شما حتی بود و پدرشما اموری. ۴۵ 45
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
و خواهر بزرگ تو سامره است که با دختران خود بطرف چپ تو ساکن می‌باشد. وخواهر کوچک تو سدوم است که با دختران خودبطرف راست تو ساکن می‌باشد. ۴۶ 46
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
اما تو درطریق های ایشان سلوک نکردی و مثل رجاسات ایشان عمل ننمودی. بلکه گویا این سهل بود که تو در همه رفتار خود از ایشان زیاده فاسد شدی.» ۴۷ 47
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
پس خداوند یهوه می‌گوید: «به حیات خودم قسم که خواهر تو سدوم و دخترانش موافق اعمال تو و دخترانت عمل ننمودند. ۴۸ 48
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
اینک گناه خواهرت سدوم این بود که تکبر وفراوانی نان و سعادتمندی رفاهیت برای او ودخترانش بود و فقیران و مسکینان را دستگیری ننمودند. ۴۹ 49
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
و مغرور شده، در حضور من مرتکب رجاسات گردیدند. لهذا چنانکه صلاح دیدم ایشان را از میان برداشتم. ۵۰ 50
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
و سامره نصف گناهانت را مرتکب نشد، بلکه تو رجاسات خودرا از آنها زیاده نمودی و خواهران خود را به تمامی رجاسات خویش که بعمل آوردی مبری ساختی. ۵۱ 51
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
پس تو نیز که بر خواهران خود حکم دادی خجالت خود را متحمل بشو. زیرا به گناهانت که در آنها بیشتر از ایشان رجاسات نمودی ایشان از تو عادلتر گردیدند. لهذا تو نیزخجل شو و رسوایی خود را متحمل باش چونکه خواهران خود را مبری ساختی. ۵۲ 52
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
و من اسیری ایشان یعنی اسیری سدوم و دخترانش و اسیری سامره و دخترانش و اسیری اسیران تو را در میان ایشان خواهم برگردانید. ۵۳ 53
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
تا خجالت خود رامتحمل شده، از هر‌چه کرده‌ای شرمنده شوی چونکه ایشان را تسلی داده‌ای. ۵۴ 54
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
و خواهرانت یعنی سدوم و دخترانش به حالت نخستین خودخواهند برگشت. و سامره و دخترانش به حالت نخستین خود خواهند برگشت. و تو و دخترانت به حالت نخستین خود خواهید برگشت. ۵۵ 55
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
اماخواهر تو سدوم در روز تکبر تو به زبانت آورده نشد. ۵۶ 56
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
قبل از آنکه شرارت تو مکشوف بشود. مثل آن زمانی که دختران ارام مذمت می‌کردند وجمیع مجاورانش یعنی دختران فلسطینیان که تورا از هر طرف خوار می‌شمردند.» ۵۷ 57
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
پس خداوند می‌فرماید که «تو قباحت ورجاسات خود را متحمل خواهی شد. ۵۸ 58
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
زیراخداوند یهوه چنین می‌گوید: به نهجی که تو عمل نمودی من با تو عمل خواهم نمود، زیرا که قسم را خوار شمرده، عهد را شکستی. ۵۹ 59
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
لیکن من عهد خود را که در ایام جوانیت با تو بستم به یادخواهم آورد و عهد جاودانی با تو استوار خواهم داشت. ۶۰ 60
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
و هنگامی که خواهران بزرگ و کوچک خود را پذیرفته باشی، آنگاه راههای خود را به یاد آورده، خجل خواهی شد. و من ایشان را به‌جای دختران به تو خواهم داد، لیکن نه از عهد تو. ۶۱ 61
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
و من عهد خود را با تو استوار خواهم ساخت وخواهی دانست که من یهوه هستم. ۶۲ 62
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
تا آنکه به یاد آورده، خجل شوی. و خداوند یهوه می‌فرماید که چون من همه کارهای تو را آمرزیده باشم، بار دیگر به‌سبب رسوایی خویش دهان خود را نخواهی گشود.» ۶۳ 63
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< حزقیال 16 >