< خروج 7 >

و خداوند به موسی گفت: «ببین تو را برفرعون خدا ساخته‌ام، و برادرت، هارون، نبی تو خواهد بود. ۱ 1
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
هرآنچه به تو امر نمایم تو آن را بگو، و برادرت هارون، آن را به فرعون بازگوید، تا بنی‌اسرائیل را از زمین خود رهایی دهد. ۲ 2
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
و من دل فرعون را سخت می‌کنم، و آیات وعلامات خود را در زمین مصر بسیار می‌سازم. ۳ 3
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
وفرعون به شما گوش نخواهد گرفت، و دست خودرا بر مصر خواهم‌انداخت، تا جنود خود، یعنی قوم خویش بنی‌اسرائیل را از زمین مصر به داوریهای عظیم بیرون آورم. ۴ 4
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
و مصریان خواهند دانست که من یهوه هستم، چون دست خود را بر مصر دراز کرده، بنی‌اسرائیل را از میان ایشان بیرون آوردم.» ۵ 5
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
و موسی و هارون چنانکه خداوند بدیشان امر فرموده بود کردند، و هم چنین عمل نمودند. ۶ 6
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
و موسی هشتاد ساله بود وهارون هشتاد و سه ساله، وقتی که به فرعون سخن‌گفتند. ۷ 7
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
پس خداوند موسی و هارون را خطاب کرده، گفت: ۸ 8
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
«چون فرعون شما را خطاب کرده، گوید معجزه‌ای برای خود ظاهر کنید، آنگاه به هارون بگو عصای خود را بگیر، و آن را پیش روی فرعون بینداز، تا اژدها شود.» ۹ 9
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
آنگاه موسی و هارون نزد فرعون رفتند، و آنچه خداوندفرموده بود کردند. و هارون عصای خود را پیش روی فرعون و پیش روی ملازمانش انداخت، واژدها شد. ۱۰ 10
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
و فرعون نیز حکیمان و جادوگران را طلبید و ساحران مصر هم به افسونهای خودچنین کردند، ۱۱ 11
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
هر یک عصای خود را انداختند و اژدها شد، ولی عصای هارون عصاهای ایشان را بلعید. ۱۲ 12
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
و دل فرعون سخت شد و ایشان رانشنید، چنانکه خداوند گفته بود. ۱۳ 13
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
و خداوند موسی را گفت: «دل فرعون سخت شده، و از رها کردن قوم ابا کرده است. ۱۴ 14
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
بامدادان نزد فرعون برو، اینک به سوی آب بیرون می‌آید، و برای ملاقات وی به کنار نهربایست، و عصا را که به مار مبدل گشت، بدست خود بگیر. ۱۵ 15
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
و او را بگو: یهوه خدای عبرانیان مرا نزد تو فرستاده، گفت: قوم مرا رها کن تا مرا درصحرا عبادت نمایند و اینک تا بحال نشنیده‌ای، ۱۶ 16
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
پس خداوند چنین می‌گوید، از این خواهی دانست که من یهوه هستم، همانا من به عصایی که در دست دارم آب نهر را می‌زنم و به خون مبدل خواهد شد. ۱۷ 17
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
و ماهیانی که در نهرند خواهندمرد، و نهر گندیده شود و مصریان نوشیدن آب نهر را مکروه خواهند داشت.» ۱۸ 18
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
و خداوند به موسی گفت: «به هارون بگوعصای خود را بگیر و دست خود را بر آبهای مصر دراز کن، بر نهرهای ایشان، و جویهای ایشان، و دریاچه های ایشان، و همه حوضهای آب ایشان، تا خون شود، و در تمامی زمین مصردر ظروف چوبی و ظروف سنگی، خون خواهدبود.» ۱۹ 19
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
و موسی و هارون چنانکه خداوند امرفرموده بود، کردند. و عصا را بلند کرده، آب نهر رابه حضور فرعون و به حضور ملازمانش زد، وتمامی آب نهر به خون مبدل شد. ۲۰ 20
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
و ماهیانی که در نهر بودند، مردند. و نهر بگندید، و مصریان از آب نهر نتوانستند نوشید، و در تمامی زمین مصرخون بود. ۲۱ 21
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
و جادوگران مصر به افسونهای خویش هم چنین کردند، و دل فرعون سخت شد، که بدیشان گوش نگرفت، چنانکه خداوند گفته بود. ۲۲ 22
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
و فرعون برگشته، به خانه خود رفت و براین نیز دل خود را متوجه نساخت. ۲۳ 23
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
و همه مصریان گرداگرد نهر برای آب خوردن حفره می‌زدند زیرا که از آب نهر نتوانستند نوشید. ۲۴ 24
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
وبعد از آنکه خداوند نهر را زده بود، هفت روزسپری شد. ۲۵ 25
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.

< خروج 7 >