< خروج 10 >

و خداوند به موسی گفت: «نزد فرعون برو زیرا که من دل فرعون و دل بندگانش را سخت کرده‌ام، تا این آیات خود را درمیان ایشان ظاهر سازم. ۱ 1
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
و تا آنچه در مصر کردم و آیات خود را که در میان ایشان ظاهر ساختم، بگوش پسرت و پسر پسرت بازگویی تا بدانید که من یهوه هستم.» ۲ 2
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
پس موسی و هارون نزد فرعون آمده، به وی گفتند: «یهوه خدای عبرانیان چنین می‌گوید: تا به کی از تواضع کردن به حضور من اباخواهی نمود؟ قوم مرا رها کن تا مرا عبادت کنند. ۳ 3
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
زیرا اگر تو از رها کردن قوم من ابا کنی، هرآینه من فردا ملخها در حدود تو فرود آورم. ۴ 4
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
که روی زمین را مستور خواهند ساخت، به حدی که زمین را نتوان دید، و تتمه آنچه رسته است که برای شمااز تگرگ باقی‌مانده، خواهند خورد، و هر درختی را که برای شما در صحرا روییده است، خواهندخورد. ۵ 5
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
و خانه تو و خانه های بندگانت وخانه های همه مصریان را پر خواهند ساخت، به مرتبه‌ای که پدرانت و پدران پدرانت از روزی که بر زمین بوده‌اند تا الیوم ندیده‌اند.» پس روگردانیده، از حضور فرعون بیرون رفت. ۶ 6
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
آنگاه بندگان فرعون به وی گفتند: «تا به کی برای ما این مرد دامی باشد؟ این مردمان را رها کن تا یهوه، خدای خود را عبادت نمایند. مگرتابحال ندانسته‌ای که مصر ویران شده است؟» ۷ 7
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
پس موسی و هارون را نزد فرعون برگردانیدند، واو به ایشان گفت: «بروید و یهوه، خدای خود راعبادت کنید، لیکن کیستند که می‌روند؟» ۸ 8
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
موسی گفت: «با جوانان و پیران خود خواهیم رفت، باپسران و دختران، و گوسفندان و گاوان خودخواهیم رفت، زیرا که ما را عیدی برای خداونداست.» ۹ 9
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
بدیشان گفت: «خداوند با شما چنین باشد، اگر شما را با اطفال شما رهایی دهم با حذرباشید زیرا که بدی پیش روی شماست! ۱۰ 10
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
نه چنین! بلکه شما که بالغ هستید رفته، خداوند راعبادت کنید، زیرا که این است آنچه خواسته بودید.» پس ایشان را از حضور فرعون بیرون راندند. ۱۱ 11
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
و خداوند به موسی گفت: «دست خود رابرای ملخها بر زمین مصر دراز کن، تا بر زمین مصربرآیند، و همه نباتات زمین را که از تگرگ مانده است، بخورند.» ۱۲ 12
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
پس موسی عصای خود را برزمین مصر دراز کرد، و خداوند تمامی آن روز، وتمامی آن شب را بادی شرقی بر زمین مصر وزانید، و چون صبح شد، باد شرقی ملخها راآورد. ۱۳ 13
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
و ملخها بر تمامی زمین مصر برآمدند، ودر همه حدود مصر نشستند، بسیار سخت که قبل از آن چنین ملخها نبود، و بعد از آن نخواهد بود. ۱۴ 14
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
و روی تمامی زمین را پوشانیدند، که زمین تاریک شد و همه نباتات زمین و همه میوه درختان را که از تگرگ باقی‌مانده بود، خوردند، به حدی که هیچ سبزی بر درخت، و نبات صحرا درتمامی زمین مصر نماند. ۱۵ 15
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
آنگاه فرعون، موسی و هارون را به زودی خوانده، گفت: «به یهوه خدای شما و به شما گناه کرده‌ام. ۱۶ 16
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
و اکنون این مرتبه فقط گناه مرا عفو فرمایید، و از یهوه خدای خود استدعا نمایید تا این موت را فقط از من برطرف نماید.» ۱۷ 17
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
پس از حضور فرعون بیرون شده، از خداوند استدعا نمود. ۱۸ 18
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
و خداوند بادغربی‌ای بسیار سخت برگردانید، که ملخها رابرداشته، آنها را به دریای قلزم ریخت، و درتمامی حدود مصر ملخی نماند. ۱۹ 19
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
اما خداونددل فرعون را سخت گردانید، که بنی‌اسرائیل رارهایی نداد. ۲۰ 20
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
و خداوند به موسی گفت: «دست خود را به سوی آسمان برافراز، تا تاریکی‌ای بر زمین مصرپدید آید، تاریکی‌ای که بتوان احساس کرد.» ۲۱ 21
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
پس موسی دست خود را به سوی آسمان برافراشت، و تاریکی غلیظ تا سه روز در تمامی زمین مصر پدید آمد. ۲۲ 22
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
و یکدیگر را نمی دیدند. و تا سه روز کسی از جای خود برنخاست، لیکن برای جمیع بنی‌اسرائیل در مسکنهای ایشان روشنایی بود. ۲۳ 23
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
و فرعون موسی را خوانده، گفت: «بروید خداوند را عبادت کنید، فقط گله هاو رمه های شما بماند، اطفال شما نیز با شمابروند.» ۲۴ 24
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
موسی گفت: «ذبایح و قربانی های سوختنی نیز می‌باید به‌دست ما بدهی، تا نزدیهوه، خدای خود بگذرانیم. ۲۵ 25
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
مواشی ما نیز با ماخواهد آمد، یک سمی باقی نخواهد ماند زیرا که از اینها برای عبادت یهوه، خدای خود می‌بایدگرفت، و تا بدانجا نرسیم، نخواهیم دانست به چه چیز خداوند را عبادت کنیم.» ۲۶ 26
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
و خداوند، دل فرعون را سخت گردانید که از رهایی دادن ایشان ابا نمود. ۲۷ 27
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
پس فرعون وی را گفت: «از حضورمن برو! و با حذر باش که روی مرا دیگر نبینی، زیرا در روزی که مرا ببینی خواهی مرد.» ۲۸ 28
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
موسی گفت: «نیکو گفتی، روی تو را دیگرنخواهم دید.» ۲۹ 29
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< خروج 10 >