< تثنیه 13 >

اگر در میان تو نبی‌ای یا بیننده خواب ازمیان شما برخیزد، و آیت یا معجزه‌ای برای شما ظاهر سازد، ۱ 1
In wani annabi ko mai mafarkai, ya bayyana a cikinku, ya kuma yi muku shelar wata alama mai banmamaki ko al’ajabi,
و آن آیت یا معجزه واقع شود که از آن تو را خبر داده، گفت خدایان غیر راکه نمی شناسی پیروی نماییم، و آنها را عبادت کنیم، ۲ 2
in kuwa alamar, ko al’ajabin da annabin ya yi faɗin ya faru, ya kuma ce, “Bari mu bi waɗansu alloli (allolin da ba ku sani ba) mu kuma yi musu sujada,”
سخنان آن نبی یا بیننده خواب را مشنو، زیرا که یهوه، خدای شما، شما را امتحان می‌کند، تا بداند که آیا یهوه، خدای خود را به تمامی دل وبه تمامی جان خود محبت می‌نمایید؟ ۳ 3
kada ku saurari kalmomin wannan annabi ko mai mafarki. Ubangiji Allahnku yana gwada ku ne don yă sani ko kuna ƙaunarsa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
یهوه خدای خود را پیروی نمایید و از او بترسید، واوامر او را نگاه دارید، و قول او را بشنوید و او راعبادت نموده، به او ملحق شوید. ۴ 4
Ubangiji Allahnku ne za ku bi, shi ne kuma za ku girmama. Ku kiyaye umarnansa, ku kuma yi masa biyayya; ku bauta masa, ku kuma manne masa.
و آن نبی یابیننده خواب کشته شود، زیرا که سخنان فتنه انگیز بر یهوه خدای شما که شما را از زمین مصر بیرون آورد، و تو را از خانه بندگی فدیه داد، گفته است تا تو را از طریقی که یهوه خدایت به توامر فرمود تا با آن سلوک نمایی، منحرف سازد، پس به این طور بدی را از میان خود دور خواهی کرد. ۵ 5
Dole a kashe wannan annabi ko mai mafarki, domin ya yi wa’azin tawaye ga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, ya fanshe ku daga ƙasar bauta; gama annabin nan ya yi ƙoƙari yă juye daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, ku bi. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
و اگر برادرت که پسر مادرت باشد یا پسر یادختر تو یا زن هم آغوش تو یا رفیقت که مثل جان تو باشد، تو را در خفا اغوا کند، و گوید که برویم وخدایان غیر را که تو و پدران تو نشناختید عبادت نماییم، ۶ 6
In ɗan’uwanka, ko ɗanka, ko’yarka, ko matar da kake ƙauna, ko abokinka na kusa, a ɓoye ya ruɗe ka, yana cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ko kai, ko kakanninka ba su sani ba,
از خدایان امتهایی که به اطراف شمامی باشند، خواه به تو نزدیک و خواه از تو دورباشند، از اقصای زمین تا اقصای دیگر آن، ۷ 7
allolin mutanen kewayenku, ko na kusa, ko na nisa, daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan),
او راقبول مکن و او را گوش مده، و چشم تو بر وی رحم نکند و بر او شفقت منما و او را پنهان مکن. ۸ 8
kada ka yarda da shi, kada ma ka saurare shi. Kada ka ji tausayinsa. Kada ka haƙura da shi, ko ka tsare shi.
البته او را به قتل رسان، دست تو اول به قتل اودراز شود و بعد دست تمامی قوم. ۹ 9
Dole ka kashe shi. Dole hannunka yă zama na farko a kisansa, sa’an nan hannuwan sauran dukan mutane.
و او را به سنگ سنگسار نما تا بمیرد، چونکه می‌خواست تو را از یهوه، خدایت، که تو را از زمین مصر ازخانه بندگی بیرون آورد، منحرف سازد. ۱۰ 10
Ku jajjefe shi da duwatsu har sai ya mutu, domin ya yi ƙoƙari yă juye ku daga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
وجمیع اسرائیلیان چون بشنوند، خواهند ترسید وبار دیگر چنین امر زشت را در میان شما مرتکب نخواهند شد. ۱۱ 11
Sa’an nan dukan Isra’ila za su ji su kuma tsorata, babu kuma wani a cikinku da zai ƙara yin irin wannan mugun abu.
اگر درباره یکی از شهرهایی که یهوه خدایت به تو به جهت سکونت می‌دهد خبر یابی، ۱۲ 12
In kuka ji an yi magana a kan wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku zauna a ciki
که بعضی پسران بلیعال از میان تو بیرون رفته، ساکنان شهر خود را منحرف ساخته، گفته اندبرویم و خدایان غیر را که نشناخته‌اید، عبادت نماییم، ۱۳ 13
cewa mugaye sun taso a cikinku, suna rikitar da mutane a birni, suna cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ba ku sani ba),
آنگاه تفحص و تجسس نموده، نیکواستفسار نما. و اینک اگر این امر، صحیح و یقین باشد که این رجاست در میان تو معمول شده است، ۱۴ 14
to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. In kuwa gaskiya ne, an kuma tabbatar wannan abin ƙyama ya faru a cikinku,
البته ساکنان آن شهر را به دم شمشیربکش و آن را با هرچه در آن است و بهایمش را به دم شمشیر هلاک نما. ۱۵ 15
dole a karkashe dukan waɗanda suke zama a wannan birni da takobi. Ku hallaka su ƙaƙaf, ku karkashe mutanen birnin da kuma dabbobinsa.
و همه غنیمت آن را در میان کوچه‌اش جمع کن و شهر را با تمامی غنیمتش برای یهوه خدایت به آتش بالکل بسوزان، و آن تا به ابد تلی خواهد بود و بار دیگربنا نخواهد شد. ۱۶ 16
Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
و از چیزهای حرام شده چیزی به‌دستت نچسبد تا خداوند از شدت خشم خود برگشته، برتو رحمت و رافت بنماید، و تو را بیفزاید بطوری که برای پدرانت قسم خورده بود. ۱۷ 17
Ba za a iske wani daga cikin abubuwan nan da aka haramta a hannuwanku ba, saboda Ubangiji yă juya daga fushinsa mai ƙuna, yă nuna jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma ƙara yawanku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku,
هنگامی که قول یهوه خدای خودرا شنیده، و همه اوامرش را که من امروز به تو امرمی فرمایم نگاه داشته، آنچه در نظر یهوه خدایت راست است، بعمل آورده باشی. ۱۸ 18
domin kun yi biyayya da Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, kuna kuma aikata abin da yake daidai a idanunsa.

< تثنیه 13 >