< دانیال 4 >

از نبوکدنصر پادشاه، به تمامی قومها و امت‌ها و زبانها که بر تمامی زمین ساکنندسلامتی شما افزون باد! ۱ 1
Daga sarki Nebukadnezzar. Zuwa ga mutane da al’ummai da kuma kowane yare, da suke zama a duniya. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku!
من مصلحت دانستم که آیات و عجایبی را که خدای تعالی به من نموده است بیان نمایم. ۲ 2
Ina murna in shaida muku game da alamu da al’ajabai waɗanda Allah Mafi Ɗaukaka ya yi ta wurina.
آیات او چه قدر بزرگ وعجایب او چه قدر عظیم است. ملکوت اوملکوت جاودانی است و سلطنت او تا ابدالاباد. ۳ 3
Alamunsa da girma suke,
من که نبوکدنصر هستم در خانه خود مطمئن ودر قصر خویش خرم می‌بودم. ۴ 4
Ni, Nebukadnezzar, ina zaune a gidana cikin fadata, ina jin daɗi ina bunkasa.
خوابی دیدم که مرا ترسانید و فکرهایم در بسترم و رویاهای سرم مرا مضطرب ساخت. ۵ 5
Na yi mafarkin da ya ba ni tsoro. A sa’ad da nake kwance a gadona, siffofi da wahayoyi da suka bi ta cikin tunanina sun firgita ni.
پس فرمانی از من صادرگردید که جمیع حکیمان بابل را به حضورم بیاورند تا تعبیر خواب را برای من بیان نمایند. ۶ 6
Don haka na ba da umarni a tattaro dukan masu hikima na Babilon su bayyana a gabana domin su fassara mini mafarkin.
آنگاه مجوسیان و جادوگران و کلدانیان ومنجمان حاضر شدند و من خواب را برای ایشان بازگفتم لیکن تعبیرش را برای من بیان نتوانستندنمود. ۷ 7
Sa’ad da masu sihiri, da masu dabo, da masanan taurari da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya fassarta mini mafarkin ba.
بالاخره دانیال که موافق اسم خدای من به بلطشصر مسمی است و روح خدایان قدوس دراو می‌باشد، درآمد و خواب را به او باز‌گفتم. ۸ 8
A ƙarshe, sai Daniyel ya zo gabana na kuma faɗa masa mafarkin. (Ana ce da shi Belteshazar, wanda aka ba shi sunan allahna kuma ruhun alloli masu tsarki suna a bisansa.)
که «ای بلطشصر، رئیس مجوسیان، چون می‌دانم که روح خدایان قدوس در تو می‌باشد و هیچ سری برای تو مشکل نیست، پس خوابی که دیده‌ام وتعبیرش را به من بگو. ۹ 9
Na ce, “Belteshazar, shugaban masu sihiri, na san ruhun alloli suna a kanka, babu wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga dai mafarkin da na yi, sai ka fassara mini.
رویاهای سرم در بسترم این بود که نظرکردم و اینک درختی در وسط زمین که ارتفاعش عظیم بود. ۱۰ 10
Waɗannan su ne wahayin da na gani a lokacin da nake kwance a gadona, na duba, a gabana kuwa ga wani itace a kafe a tsakiyar duniya, yana da tsawo ƙwarai.
این درخت بزرگ و قوی گردید وبلندیش تا به آسمان رسید و منظرش تا اقصای تمامی زمین بود. ۱۱ 11
Itacen ya yi girma ya kuma yi ƙarfi, har tsayinsa ya taɓa sarari sama; ana iya ganinsa a ko’ina a duniya.
برگهایش جمیل و میوه‌اش بسیار و آذوقه برای همه در آن بود. حیوانات صحرا در زیر آن سایه گرفتند و مرغان هوا برشاخه هایش ماوا گزیدند و تمامی بشر از آن پرورش یافتند. ۱۲ 12
Ganyayensa suna da kyau, yana da’ya’ya jingim, abinci kuma domin kowa da kowa. A ƙarƙashinsa namun jeji suke samun wurin hutawa, kuma tsuntsayen sama suna zaune a bisa rassansa; daga cikinsa kowace halitta take cin abinci.
در رویاهای سرم در بسترم نظر کردم و اینک پاسبانی و مقدسی از آسمان نازل شد، ۱۳ 13
“A cikin wahayin da gani sa’ad da nake kwance a kan gadona, Na duba, a gabana kuwa ga wani ɗan saƙo, mai tsarki, yana saukowa daga sama.
که به آواز بلند ندا درداد و چنین گفت: درخت را ببرید و شاخه هایش را قطع نمایید و برگهایش را بیفشانید و میوه هایش راپراکنده سازید تا حیوانات از زیرش و مرغان ازشاخه هایش آواره گردند. ۱۴ 14
Sai ya yi kira da babbar murya ya ce, ‘A sare itacen a kuma yayyanka rassansa; a karkaɗe ganyensa a kuma warwatsar da’ya’yansa. Bari dabbobi su tashi daga ƙarƙashinsa da kuma tsuntsayen da suke a rassansa.
لیکن کنده ریشه هایش را با بند آهن و برنج در زمین در میان سبزه های صحرا واگذارید و از شبنم آسمان ترشود و نصیب او از علف زمین با حیوانات باشد. ۱۵ 15
Amma a bar kututturen da kuma saiwoyinsa, a daure shi da ƙarfe da kuma tagulla, a bar shi a cikin ƙasa, a cikin ciyayin filaye. “‘Bari yă jiƙu da raɓar, bari yă zauna cikin dabbobi tare da tsire-tsiren duniya.
دل او از انسانیت تبدیل شود و دل حیوان را به او بدهند و هفت زمان براو بگذرد. ۱۶ 16
Bari a canja tunaninsa irin na mutane a ba shi tunani irin na dabbobi, har sau bakwai su wuce a kansa.
این امر ازفرمان پاسبانان شده و این حکم از کلام مقدسین گردیده است تا زندگان بدانند که حضرت متعال بر ممالک آدمیان حکمرانی می‌کند و آن را بهرکه می‌خواهد می‌دهد و پست‌ترین مردمان را بر آن نصب می‌نماید. ۱۷ 17
“‘An sanar da wannan matsayi ne ta bakin’yan saƙo, masu tsarki ne kuwa suka sanar da hukuncin, domin masu rai su sani Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a bisa kowane mulkin mutane, yakan kuma ba wa duk wanda ya ga dama, yakan sanya talaka yă zama sarki.’
این خواب را من که نبوکدنصرپادشاه هستم دیدم و تو‌ای بلطشصر تعبیرش رابیان کن زیرا که تمامی حکیمان مملکتم نتوانستندمرا از تعبیرش اطلاع دهند، اما تو می‌توانی چونکه روح خدایان قدوس در تو می‌باشد.» ۱۸ 18
“Wannan shi ne mafarkin da ni, Nebukadnezzar, na yi. Yanzu Belteshazar, sai ka faɗa mini abin da yake nufi, domin babu wani a cikin masu hikima a mulkina da ya iya fassara mini shi. Amma za ka iya, domin ruhun alloli masu tsarki yana a bisanka.”
آنگاه دانیال که به بلطشصر مسمی می‌باشد، ساعتی متحیر ماند و فکرهایش او رامضطرب ساخت. پس پادشاه متکلم شده، گفت: «ای بلطشصر خواب و تعبیرش تو را مضطرب نسازد.» بلطشصر در جواب گفت: «ای آقای من! خواب از برای دشمنانت و تعبیرش از برای خصمانت باشد. ۱۹ 19
Sai Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) ya tsaya zugum na ɗan lokaci, tunaninsa ya ba shi tsoro. Saboda haka sarki ya ce, “Belteshazar, kada ka bar mafarkin ko ma’anarsa ta tayar maka da hankali.” Belteshazar ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, in dai har mafarkin zai tsaya a kan abokan gābanka da ma’anarsa kuma ta faɗa kan maƙiyan!
درختی که دیدی که بزرگ وقوی گردید و ارتفاعش تا به آسمان رسید ومنظرش به تمامی زمین ۲۰ 20
Itacen da ka gani; wanda ya yi girma da ƙarfe, da tsayinsa ya taɓa sararin sama, wanda ana ganinsa ko’ina a duniya,
و برگهایش جمیل و میوه‌اش بسیار و آذوقه برای همه در آن بود وحیوانات صحرا زیرش ساکن بودند و مرغان هوادر شاخه هایش ماوا گزیدند، ۲۱ 21
wanda ganyayensa masu kyau ne yana da’ya’yan itace da yawa, wanda yake ba da abinci ga duka, yana ba da wurin hutu ga namun jeji, kuma rassansa suna ɗauke da sheƙar tsuntsayen sama.
‌ای پادشاه آن درخت تو هستی زیرا که تو بزرگ و قوی گردیده‌ای و عظمت تو چنان افزوده شده است که به آسمان رسیده و سلطنت تو تا به اقصای زمین. ۲۲ 22
Ya sarki kai ne itacen nan! Ka yi girma da ƙarfi; girmanka kuma ta kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko’ina a duniya.
و چونکه پادشاه پاسبانی و مقدسی را دید که ازآسمان نزول نموده، گفت: درخت را ببرید و آن راتلف سازید، لیکن کنده ریشه هایش را با بند آهن و برنج در زمین در میان سبزه های صحراواگذارید و از شبنم آسمان تر شود و نصیبش باحیوانات صحرا باشد تا هفت زمان بر آن بگذرد، ۲۳ 23
“Ya sarki ka ga ɗan saƙon mai tsarkin nan, yana saukowa daga sama yana cewa, ‘A sare itacen a hallaka shi, amma a bar kututturensa daure da ƙarfe da tagulla, a bar shi can a ɗanyar ciyawar filaye, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namun jeji har shekara bakwai.’
‌ای پادشاه تعبیر این است و فرمان حضرت متعال که بر آقایم پادشاه وارد شده است همین است، ۲۴ 24
“Ga fassarar, ya sarki, wannan ita ce doka wadda Mafi Ɗaukaka ya bayar a kan ranka yă daɗe, sarkina.
که تو را از میان مردمان خواهند راند ومسکن تو با حیوانات صحرا خواهد بود و تو رامثل گاوان علف خواهند خورانید و تو را از شبنم آسمان تر خواهند ساخت و هفت زمان بر توخواهد گذشت تا بدانی که حضرت متعال برممالک آدمیان حکمرانی می‌کند و آن را بهر‌که می‌خواهد عطا می‌فرماید. ۲۵ 25
Za a kore ka daga cikin mutane, za ka kuma zauna cikin namun jeji; za ka ci ciyawa kamar shanu, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cif sa’an nan za ka sani cewa Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
و چون گفتند که کنده ریشه های درخت را واگذارید، پس سلطنت تو برایت برقرار خواهد ماند بعد از آنکه دانسته باشی که آسمانها حکمرانی می‌کنند. ۲۶ 26
Umarni na barin kututturen itacen da saiwoyinsa yana nufin cewa za a maido maka da mulkinka a lokacin da ka gane cewa Mai sama ne yake mulki.
لهذا‌ای پادشاه نصیحت من تو را پسند آید و گناهان خودرا به عدالت و خطایای خویش را به احسان نمودن بر فقیران فدیه بده که شاید باعث طول اطمینان تو باشد.» ۲۷ 27
Saboda haka, ya sarki, ina roƙonka ka karɓi shawarar da zan ba ka; ka furta zunubanka ta wurin yin abin da yake daidai. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulaƙantawa, wataƙila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.”
این همه بر نبوکدنصرپادشاه واقع شد. ۲۸ 28
Duk wannan kuwa ya faru da sarki Nebukadnezzar.
بعد از انقضای دوازده ماه او بالای قصرخسروی در بابل می‌خرامید. ۲۹ 29
Bayan wata goma sha biyu, a sa’ad da sarki yake takawa a bisan saman ɗakin fadar Babilon,
و پادشاه متکلم شده، گفت: «آیا این بابل عظیم نیست که من آن را برای خانه سلطنت به توانایی قوت و حشمت جلال خود بنا نموده‌ام؟» ۳۰ 30
sai ya ce, “Ba wannan ita ce Babilon babba da na gina domin wurin zaman sarautar Babilon, da ikona kuma domin ɗaukakar darajata ba?”
این سخن هنوز برزبان پادشاه بود که آوازی از آسمان نازل شده، گفت: «ای پادشاه نبوکدنصر به تو گفته می‌شود که سلطنت از تو گذشته است. ۳۱ 31
Tun kalmomin suna cikin bakinsa sai ya ji murya daga sama tana cewa, “Wannan shi ne abin da aka zartar a kanka, Sarki Nebukadnezzar. An karɓe ikon mulkinka.
و تو را از میان مردم خواهند راند و مسکن تو با حیوانات صحراخواهد بود و تو را مثل گاوان علف خواهندخورانید و هفت زمان بر تو خواهد گذشت تابدانی که حضرت متعال بر ممالک آدمیان حکمرانی می‌کند و آن را بهر‌که می‌خواهدمی دهد.» ۳۲ 32
Za a kore ka daga cikin mutane za ka kuma yi rayuwa tare da namun jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cif, sa’an nan za ka gane Mafi Ɗaukaka ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.”
در همان ساعت این امر بر نبوکدنصر واقع شد و از میان مردمان رانده شده، مثل گاوان علف می‌خورد و بدنش از شبنم آسمان تر می‌شد تامویهایش مثل پرهای عقاب بلند شد وناخنهایش مثل چنگالهای مرغان گردید. ۳۳ 33
Nan da nan abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar tabbatarsa ya cika. Aka kore shi daga cikin mutane ya kuma shiga cin ciyawa kamar shanu. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar fikafikan gaggafa, kumbarsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.
و بعد از انقضای آن ایام من که نبوکدنصرهستم، چشمان خود را بسوی آسمان برافراشتم و عقل من به من برگشت و حضرت متعال رامتبارک خواندم و حی سرمدی را تسبیح و حمدگفتم زیرا که سلطنت او سلطنت جاودانی وملکوت او تا ابدالاباد است. ۳۴ 34
A ƙarshen waɗannan kwanaki, ni, Nebukadnezzar, na ɗaga idanuna sama, sai hankalina ya komo mini. Na kuwa yabi Maɗaukaki, na girmama shi, na ɗaukaka shi wanda yake rayayye har abada.
و جمیع ساکنان جهان هیچ شمرده می‌شوند و با جنود آسمان وسکنه جهان بر وفق اراده خود عمل می‌نماید وکسی نیست که دست او را باز‌دارد یا او را بگویدکه چه می‌کنی. ۳۵ 35
Dukan mutanen duniya
در همان زمان عقل من به من برگشت و به جهت جلال سلطنت من حشمت وزینتم به من باز داده شد و مشیرانم و امرایم مراطلبیدند و بر سلطنت خود استوار گردیدم وعظمت عظیمی بر من افزوده شد. ۳۶ 36
A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana.’Yan majalisata da fadawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.
الان من که نبوکدنصر هستم پادشاه آسمانها را تسبیح وتکبیر و حمد می‌گویم که تمام کارهای او حق و طریق های وی عدل است و کسانی که با تکبر راه می‌روند، او قادر است که ایشان را پست نماید. ۳۷ 37
Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin sama, ina waƙa ina kuma darjanta shi, saboda dukan abin da ya yi mini, mai kyau ne kuma dukan hanyoyinsa gaskiya ne. Kuma duk masu tafiya da girman kai zai ƙasƙantar da su.

< دانیال 4 >