< عاموس 9 >

خداوند را دیدم که نزد مذبح ایستاده بود وگفت: «تاجهای ستونها را بزن تا آستانه ها بلرزد و آنها را بر سر همه مردم بینداز وباقی ماندگان ایشان را به شمشیر خواهم کشت وفراری‌ای از ایشان نخواهد گریخت وباقی‌مانده‌ای از ایشان نخواهد رست. ۱ 1
Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
اگر به هاویه فرو روند، دست من ایشان را از آنجاخواهد گرفت و اگر به آسمان صعود نمایند، ایشان را از آنجا فرود خواهم آورد. (Sheol h7585) ۲ 2
Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
و اگر به قله کرمل پنهان شوند ایشان را تفتیش کرده، از آنجاخواهم گرفت و اگر از نظر من در قعر دریاخویشتن را مخفی نمایند، در آنجا مار را امرخواهم فرمود که ایشان را بگزد. ۳ 3
Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
و اگر پیش دشمنان خود به اسیری روند شمشیر را در آنجاامر خواهم فرمود تا ایشان را بکشد و نظر خود رابر ایشان برای بدی خواهم داشت و نه برای نیکویی. ۴ 4
Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
خداوند یهوه صبایوت که زمین را لمس می‌کند و آن گداخته می‌گردد و همه ساکنانش ماتم می‌گیرند و تمامش مثل نهر برمی آید و مانندنیل مصر فرو می‌نشیند؛ ۵ 5
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
آن که غرفه های خود رادر آسمان بنا می‌کند و طاقهای خود را بر زمین بنیاد می‌نهد و آبهای دریا را ندا در‌داده، آنها را به روی زمین می‌ریزد نام او یهوه می‌باشد. ۶ 6
shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
خداوندمی گوید: «ای بنی‌اسرائیل آیا شما برای من مثل پسران حبشیان نیستید؟ آیا اسرائیل را از زمین مصر و فلسطینیان را از کفتور و ارامیان را از قیربرنیاوردم؟» ۷ 7
“Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
اینک چشمان خداوند یهوه بر مملکت گناهکار می‌باشد و من آن را از روی زمین هلاک خواهم ساخت لیکن خداوند می‌گوید که «خاندان یعقوب را بالکل هلاک نخواهم ساخت. ۸ 8
“Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
زیرا اینک من امر فرموده، خاندان اسرائیل را درمیان همه امت‌ها خواهم بیخت، چنانکه غله در غربال بیخته می‌شود و دانه‌ای بر زمین نخواهدافتاد. ۹ 9
“Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
جمیع گناهکاران قوم من که می‌گویند بلابه ما نخواهد رسید و ما را درنخواهد گرفت، به شمشیر خواهند مرد. ۱۰ 10
Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
در آن روز خیمه داود راکه افتاده است برپا خواهم نمود و شکافهایش رامرمت خواهم کرد و خرابیهایش را برپا نموده، آن را مثل ایام سلف بنا خواهم کرد. ۱۱ 11
“A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
تا ایشان بقیه ادوم و همه امت‌ها را که اسم من بر ایشان نهاده شده است، به تصرف آورند.» خداوند که این رابجا می‌آورد تکلم نموده است. ۱۲ 12
domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
اینک خداوند می‌گوید: «ایامی می‌آید که شیارکننده به دروکننده خواهد رسید وپایمال کننده انگور به‌کارنده تخم. و کوهها عصیرانگور را خواهد چکانید و تمامی تلها به سیلان خواهد آمد. ۱۳ 13
“Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
و اسیری قوم خود اسرائیل راخواهم برگردانید و شهرهای مخروب را بنانموده، در آنها ساکن خواهند شد و تاکستانهاغرس کرده، شراب آنها را خواهند نوشید و باغهاساخته، میوه آنها را خواهند خورد.» ۱۴ 14
Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
و یهوه خدایت می‌گوید: «من ایشان را درزمین ایشان غرس خواهم نمود و بار دیگر اززمینی که به ایشان داده‌ام کنده نخواهند شد.» ۱۵ 15
Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.

< عاموس 9 >