< دوم سموئیل 7 >
و واقع شد چون پادشاه در خانه خود نشسته، و خداوند او را از جمیع دشمنانش از هر طرف آرامی داده بود، | ۱ 1 |
Bayan sarki ya kama zama a fadansa Ubangiji kuma ya hutashe shi daga dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi,
که پادشاه به ناتان نبی گفت: «الان مرا میبینی که در خانه سرو آزادساکن میباشم، و تابوت خدا در میان پردهها ساکن است.» | ۲ 2 |
sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Allah yana zaune a tenti.”
ناتان به پادشاه گفت: «بیا و هرآنچه دردلت باشد معمول دار زیرا خداوند با توست.» | ۳ 3 |
Natan ya amsa wa sarki ya ce, “Duk abin da yake a zuciyarka, sai ka yi, gama Ubangiji yana tare da kai.”
و در آن شب واقع شد که کلام خداوند به ناتان نازل شده، گفت: | ۴ 4 |
A daren nan maganar Ubangiji ta zo wa Natan cewa,
«برو و به بنده من داودبگو، خداوند چنین میگوید: آیا تو خانهای برای سکونت من بنا میکنی؟ | ۵ 5 |
“Je ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, kai ne za ka gina mini gida in zauna?
زیرا از روزی که بنیاسرائیل را از مصر بیرون آوردم تا امروز، درخانهای ساکن نشدهام بلکه در خیمه و مسکن گردش کردهام. | ۶ 6 |
Ban taɓa zama a gida ba tun daga ranar da na fito da Isra’ilawa daga Masar har yă zuwa yau. Ina dai kai da kawowa a tenti, a matsayin mazaunina.
و به هر جایی که با جمیع بنیاسرائیل گردش کردم آیا به احدی از داوران اسرائیل که برای رعایت قوم خود، اسرائیل، مامور داشتم، سخنی گفتم که چرا خانهای از سروآزاد برای من بنا نکردید؟ | ۷ 7 |
A cikin kaiwa da kawowar da nake yi cikin dukan Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani shugabanninsu wanda na umarta su lura da mutanena Isra’ila, “Don me ba ku gina mini mazauni da katakon al’ul ba?”’
و حال به بنده من، داود چنین بگو که یهوه صبایوت چنین میگوید: من تو را از چراگاه از عقب گوسفندان گرفتم تاپیشوای قوم من، اسرائیل، باشی. | ۸ 8 |
“Yanzu, ka gaya wa bawana Dawuda ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauko ka daga makiyaya, daga kuma garken tumaki ka zama sarki bisan mutane Isra’ila.
و هر جایی که میرفتی من با تو میبودم و جمیع دشمنانت را ازحضور تو منقطع ساختم، و برای تو اسم بزرگ مثل اسم بزرگانی که بر زمینند، پیدا کردم. | ۹ 9 |
Na kasance tare da kai duk inda ka tafi, na kuma kawar da dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka yă shahara kamar sunayen shahararrun mutanen duniya.
و به جهت قوم خود، اسرائیل، مکانی تعیین کردم وایشان را غرس نمودم تا در مکان خویش ساکن شده، باز متحرک نشوند، و شریران، دیگر ایشان را مثل سابق ذلیل نسازند. | ۱۰ 10 |
Zan kuma tanada wa mutanena Isra’ila wuri, in kuma dasa su yadda za su kasance da gida kansu ba tare da an ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba,
و مثل روزهایی که داوران را بر قوم خود، اسرائیل، تعیین نموده بودم و تو را از جمیع دشمنانت آرامی دادم، و خداوندتو را خبر میدهد که خداوند برای تو خانهای بناخواهد نمود. | ۱۱ 11 |
yadda suka yi tun lokacin da na naɗa shugabanni bisan mutanena Isra’ila, zan kuma hutashe ka daga hannun abokan gābanka. “‘Ubangiji ya furta maka cewa Ubangiji kansa zai kafa maka gida.
زیرا روزهای تو تمام خواهدشد و با پدران خود خواهی خوابید و ذریت تو راکه از صلب تو بیرون آید، بعد از تو استوار خواهم ساخت، و سلطنت او را پایدار خواهم نمود. | ۱۲ 12 |
Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
او برای اسم من خانهای بنا خواهد نمود وکرسی سلطنت او را تا به ابد پایدار خواهم ساخت. | ۱۳ 13 |
Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
من او را پدر خواهم بود و او مرا پسرخواهد بود، و اگر او گناه ورزد، او را با عصای مردمان و به تازیانه های بنی آدم تادیب خواهم نمود. | ۱۴ 14 |
Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
ولیکن رحمت من از او دور نخواهد شد، به طوری که آن را از شاول دور کردم که او را ازحضور تو رد ساختم. | ۱۵ 15 |
Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
و خانه و سلطنت تو، به حضورت تا به ابد پایدار خواهد شد، و کرسی توتا به ابد استوار خواهد ماند.» | ۱۶ 16 |
Gidanka da kuma masarautarka za su dawwama har abada a gabana; gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’”
برحسب تمامی این کلمات و مطابق تمامی اینرویا ناتان به داودتکلم نمود. | ۱۷ 17 |
Natan ya gaya wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.
و داود پادشاه داخل شده، به حضورخداوند نشست و گفت: «ای خداوند یهوه، من کیستم و خاندان من چیست که مرا به این مقام رسانیدی؟ | ۱۸ 18 |
Sa’an nan Sarki Dawuda ya je ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ko gidana, har da ka ɗaga mu zuwa wannan matsayi?
و این نیز در نظر توای خداوند یهوه امر قلیل نمود زیرا که درباره خانه بنده ات نیزبرای زمان طویل تکلم فرمودی. و آیا اینای خداوند یهوه عادت بنی آدم است؟ | ۱۹ 19 |
Har ya zama kamar wannan bai isa ba a gabanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka kuma yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Haka ka saba yi da mutane, ya Ubangiji Mai Iko Duka?
و داوددیگر به تو چه تواند گفت زیرا که توای خداوندیهوه، بنده خود را میشناسی، | ۲۰ 20 |
“Me kuma Dawuda zai ce maka? Gama ka san bawanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka.
و برحسب کلام خود و موافق دل خود تمامی این کارهای عظیم را بجا آوردی تا بنده خود را تعلیم دهی. | ۲۱ 21 |
Gama saboda maganarka da kuma bisa ga nufinka, ka aikata wannan babban abu, ka kuma sanar da bawanka.
بنابرینای یهوه خدا، تو بزرگ هستی زیراچنانکه به گوشهای خود شنیدهایم مثل تو کسی نیست و غیر از تو خدایی نیست. | ۲۲ 22 |
“Kai mai girma ne, ya Ubangiji Mai Iko Duka! Babu wani kamar ka, babu kuma wani Allah sai kai; kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
و مثل قوم تواسرائیل کدامیک امت بر روی زمین است که خدابیاید تا ایشان را فدیه داده، برای خویش قوم بسازد، و اسمی برای خود پیدا نماید، و چیزهای عظیم و مهیب برای شما و برای زمین خود بجاآورد به حضور قوم خویش که برای خود از مصرو از امتها و خدایان ایشان فدیه دادی. | ۲۳ 23 |
Wane ne kuma yake kamar da mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allah ya fita don yă kuɓutar wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa da kuma al’amuran banmamaki ta wurin korin al’ummai da allolinsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar?
و قوم خود اسرائیل را برای خود استوار ساختی، تاایشان تا به ابد قوم تو باشند، و توای یهوه، خدای ایشان شدی. | ۲۴ 24 |
Ka kafa mutanenka Isra’ila kamar naka na kanka har abada, kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
و الانای یهوه خدا، کلامی را که درباره بنده خود و خانهاش گفتی تا به ابد استوارکن، و برحسب آنچه گفتی، عمل نما. | ۲۵ 25 |
“Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa. Ka yi kamar yadda ka alkawarta,
و اسم توتا به ابد معظم بماند، تا گفته شود که یهوه صبایوت، خدای اسرائیل است، و خاندان بنده ات داود به حضور تو پایدار بماند. | ۲۶ 26 |
domin sunanka yă kasance da girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah ne a bisa Isra’ila!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
زیرا توای یهوه صبایوت، خدای اسرائیل، به بنده خوداعلان نموده، گفتی که برای تو خانهای بنا خواهم نموده، بنابرین بنده تو جرات کرده است که این دعا را نزد تو بگوید. | ۲۷ 27 |
“Ya Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka bayyana wa bawanka cewa, ‘Zan gina maka gida.’ Saboda haka bawanka ya sami ƙarfin hali yă miƙa maka wannan addu’a.
و الانای خداوند یهوه توخدا هستی و کلام تو صدق است و این نیکویی رابه بنده خود وعده دادهای. | ۲۸ 28 |
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai Allah ne! Maganarka da aminci take, ka kuma yi wa bawanka waɗannan abubuwa masu kyau.
و الان احسان فرموده، خاندان بنده خود را برکت بده تا آنکه درحضورت تا به ابد بماند، زیرا که توای خداوندیهوه گفتهای و خاندان بنده ات از برکت تو تا به ابدمبارک خواهد بود.» | ۲۹ 29 |
In ya gamshe ka, bari ka albarkaci gidan bawanka don yă dawwama a gabanka har abada; gama kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka riga ka yi magana, kuma saboda kai ka sa albarka ga gidan bawanka, lalle zai kasance da albarka har abada.”