< دوم سموئیل 20 >

و اتفاق مرد بلیعال، مسمی به شبع بن بکری بنیامینی در آنجا بود و کرنا رانواخته، گفت که «ما را در داود حصه‌ای نیست، وبرای ما در پسر یسا نصیبی نی، ای اسرائیل! هرکس به خیمه خود برود.» ۱ 1
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
و تمامی مردان اسرائیل از متابعت داود به متابعت شبع ابن بکری برگشتند، اما مردان یهودا از اردن تا اورشلیم، پادشاه را ملازمت نمودند. ۲ 2
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
و داود به خانه خود در اورشلیم آمد، وپادشاه ده زن متعه را که برای نگاهبانی خانه خودگذاشته بود، گرفت و ایشان را در خانه محروس نگاه داشته، پرورش داد، اما نزد ایشان داخل نشدو ایشان تا روز مردن در حالت بیوگی محبوس بودند. ۳ 3
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
و پادشاه به عماسا گفت: «مردان یهودا را درسه روز نزد من جمع کن و تو در اینجا حاضر شو.» ۴ 4
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
پس عماسا رفت تا یهودا را جمع کند، اما اززمانی که برایش تعیین نموده بود تاخیر کرد. ۵ 5
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
وداود به ابیشای گفت: «الان شبع بن بکری بیشتر ازابشالوم به ما ضرر خواهد رسانید؛ پس بندگان آقایت را برداشته، او را تعاقب نما مبادا شهرهای حصاردار برای خود پیدا کند و از نظر ما رهایی یابد.» ۶ 6
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
و کسان یوآب و کریتیان و فلیتیان و جمیع شجاعان از عقب او بیرون رفتند، و به جهت تعاقب نمودن شبع بن بکری از اورشلیم روانه شدند. ۷ 7
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
و چون ایشان نزد سنگ بزرگی که درجبعون است رسیدند، عماسا به استقبال ایشان آمد. و یوآب ردای جنگی دربرداشت و بر آن بندشمشیری که در غلافش بود، بر کمرش بسته، و چون می‌رفت شمشیر از غلاف افتاد. ۸ 8
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
و یوآب به عماسا گفت: «ای برادرم آیا به سلامت هستی؟» ویوآب ریش عماسا را به‌دست راست خود گرفت تا او را ببوسد. ۹ 9
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
و عماسا به شمشیری که دردست یوآب بود، اعتنا ننمود. پس او آن را به شکمش فرو برد که احشایش به زمین ریخت و اورا دوباره نزد و مرد. ۱۰ 10
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
و یکی از خادمان یوآب نزدوی ایستاده، گفت: «هرکه یوآب را می‌خواهد وهرکه به طرف داود است، در عقب یوآب بیاید.» ۱۱ 11
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
و عماسا در میان راه در خونش می‌غلطید، وچون آن شخص دید که تمامی قوم می‌ایستند، عماسا را از میان راه در صحرا کشید و لباسی بر اوانداخت زیرا دید که هر‌که نزدش می‌آید، می‌ایستد. ۱۲ 12
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
پس چون از میان راه برداشته شد، جمیع مردان در عقب یوآب رفتند تا شبع بن بکری را تعاقب نمایند. ۱۳ 13
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
و او از جمیع اسباط اسرائیل تا آبل و تا بیت معکه و تمامی بیریان عبور کرد، و ایشان نیز جمع شده، او را متابعت کردند. ۱۴ 14
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
و ایشان آمده، او رادر آبل بیت معکه محاصره نمودند و پشته‌ای دربرابر شهر ساختند که در برابر حصار برپا شد، وتمامی قوم که با یوآب بودند، حصار را می‌زدند تاآن را منهدم سازند. ۱۵ 15
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
و زنی حکیم از شهر صدادرداد که بشنوید: «به یوآب بگویید: اینجا نزدیک بیا تا با تو سخن گویم.» ۱۶ 16
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
و چون نزدیک وی شد، زن گفت که «آیا تو یوآب هستی؟» او گفت: «من هستم.» وی را گفت: «سخنان کنیز خود را بشنو.» او گفت: «می‌شنوم.» ۱۷ 17
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
پس زن متکلم شده، گفت: «در زمان قدیم چنین می‌گفتند که هرآینه درآبل می‌باید مشورت بجویند و همچنین هر امری را ختم می‌کردند. ۱۸ 18
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
من در اسرائیل سالم و امین هستم و تو می‌خواهی شهری و مادری را دراسرائیل خراب کنی، چرا نصیب خداوند را بالکل هلاک می‌کنی؟» ۱۹ 19
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
پس یوآب در جواب گفت: «حاشا از من حاشا از من! که هلاک یا خراب نمایم. ۲۰ 20
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
کار چنین نیست بلکه شخصی مسمی به شبع بن بکری از کوهستان افرایم دست خود را برداود پادشاه بلند کرده است. او را تنها بسپارید واز نزد شهر خواهم رفت.» زن در جواب یوآب گفت: «اینک سر او را از روی حصار نزد توخواهند انداخت.» ۲۱ 21
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
پس آن زن به حکمت خودنزد تمامی قوم رفت و ایشان سر شبع بن بکری رااز تن جدا کرده، نزد یوآب انداختند و او کرنا رانواخته، ایشان از نزد شهر، هر کس به خیمه خودمتفرق شدند. و یوآب به اورشلیم نزد پادشاه برگشت. ۲۲ 22
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
و یوآب، سردار تمامی لشکر اسرائیل بود، و بنایاهو ابن یهویاداع سردار کریتیان و فلیتیان بود. ۲۳ 23
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
و ادورام سردار باجگیران و یهوشافاط بن اخیلود وقایع نگار، ۲۴ 24
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
و شیوا کاتب و صادوق وابیاتار، کاهن بودند، ۲۵ 25
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
و عیرای یائیری نیز کاهن داود بود. ۲۶ 26
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.

< دوم سموئیل 20 >