< دوم پادشاهان 20 >

در آن ایام، حزقیا بیمار و مشرف به موت شد و اشعیا ابن آموص نبی نزدوی آمده، او را گفت: «خداوند چنین می‌گوید: تدارک خانه خود را ببین زیرا که می‌میری و زنده نخواهی ماند.» ۱ 1
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
آنگاه او روی خود را به سوی دیوار برگردانید و نزد خداوند دعا نموده، گفت: ۲ 2
Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
«ای خداوند مسالت اینکه بیاد آوری که چگونه به حضور تو به امانت و به دل کامل سلوک نموده‌ام و آنچه در نظر تو پسند بوده است، بجا آورده‌ام.» پس حزقیا زارزار بگریست. ۳ 3
“Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
و واقع شد قبل از آنکه اشعیا از وسط شهربیرون رود، که کلام خداوند بر وی نازل شده، گفت: ۴ 4
Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
«برگرد و به پیشوای قوم من حزقیا بگو: خدای پدرت، داود چنین می‌گوید: دعای تو راشنیدم و اشکهای تو را دیدم. اینک تو را شفاخواهم داد و در روز سوم به خانه خداوند داخل خواهی شد. ۵ 5
“Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
و من بر روزهای تو پانزده سال خواهم افزود، و تو را و این شهر را از دست پادشاه آشور خواهم رهانید، و این شهر را به‌خاطر خود و به‌خاطر بنده خود، داود حمایت خواهم کرد.» ۶ 6
Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
و اشعیا گفت که «قرصی از انجیربگیرید.» و ایشان آن را گرفته، بر دمل گذاشتند که شفا یافت. ۷ 7
Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
و حزقیا به اشعیا گفت: «علامتی که خداوند مرا شفا خواهد بخشید و در روز سوم به خانه خداوند خواهم برآمد، چیست؟» ۸ 8
Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
و اشعیا گفت: «علامت از جانب خداوند که خداوند این کلام راکه گفته است، بجا خواهد آورد، این است: آیاسایه ده درجه پیش برود یا ده درجه برگردد؟» ۹ 9
Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
حزقیا گفت: «سهل است که سایه ده درجه پیش برود. نی، بلکه سایه ده درجه به عقب برگردد.» ۱۰ 10
“Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
پس اشعیای نبی از خداوند استدعانمود و سایه را از درجاتی که بر ساعت آفتابی آحاز پایین رفته بود، ده درجه برگردانید. ۱۱ 11
Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
و در آن زمان، مرودک بلدان بن بلدان، پادشاه بابل، رسایل و هدیه نزد حزقیا فرستاد زیراشنیده بود که حزقیا بیمار شده است. ۱۲ 12
A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
و حزقیاایشان را اجابت نمود و تمامی خانه خزانه های خود را از نقره و طلا و عطریات و روغن معطر وخانه اسلحه خویش و هرچه را که در خزاین اویافت می‌شد، به ایشان نشان داد، و در خانه‌اش ودر تمامی مملکتش چیزی نبود که حزقیا آن را به ایشان نشان نداد. ۱۳ 13
Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
پس اشعیای نبی نزد حزقیای پادشاه آمده، وی را گفت: «این مردمان چه گفتند؟ و نزد تو از کجا آمدند؟» حزقیا جواب داد: «ازجای دور، یعنی از بابل آمده‌اند.» ۱۴ 14
Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
او گفت: «درخانه تو چه دیدند؟» حزقیا جواب داد: «هرچه درخانه من است، دیدند و چیزی در خزاین من نیست که به ایشان نشان ندادم.» ۱۵ 15
Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
پس اشعیا به حزقیا گفت: «کلام خداوند رابشنو: ۱۶ 16
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
اینک روزها می‌آید که هرچه در خانه توست و آنچه پدرانت تا امروز ذخیره کرده‌اند، به بابل برده خواهد شد. و خداوند می‌گوید که چیزی باقی نخواهد ماند. ۱۷ 17
Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
و بعضی از پسرانت را که از تو پدید آیند و ایشان را تولید نمایی، خواهند گرفت و در قصر پادشاه بابل، خواجه خواهند شد.» ۱۸ 18
Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
حزقیا به اشعیا گفت: «کلام خداوند که گفتی نیکوست.» و دیگر گفت: «هرآینه در ایام من سلامتی و امان خواهد بود.» ۱۹ 19
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
و بقیه وقایع حزقیا و تمامی تهور او وحکایت حوض و قناتی که ساخت و آب را به شهر آورد، آیا در کتاب تواریخ ایام پادشاهان یهودا مکتوب نیست؟ ۲۰ 20
Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
پس حزقیا با پدران خود خوابید و پسرش، منسی به‌جایش سلطنت نمود. ۲۱ 21
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.

< دوم پادشاهان 20 >