< دوم پادشاهان 19 >

و واقع شد که چون حزقیای پادشاه این را شنید، لباس خود را چاک زده، وپلاس پوشیده، به خانه خداوند داخل شد. ۱ 1
Da sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakketa tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya shiga haikalin Ubangiji.
والیاقیم، ناظر خانه و شبنه کاتب و مشایخ کهنه راملبس به پلاس نزد اشعیا ابن آموص نبی فرستاده، ۲ 2
Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna marubuci da shugabannin firistoci, dukansu sanye da tufafin makoki, zuwa wurin annabi Ishaya ɗan Amoz.
به وی گفتند: «حزقیا چنین می‌گوید که «امروزروز تنگی و تادیب و اهانت است زیرا که پسران به فم رحم رسیده‌اند و قوت زاییدن نیست. ۳ 3
Suka ce masa, “Hezekiya ya ce, yau ranar wahala ce, da ta cin mutunci, da ta shan kunya, ga shi,’ya’ya suna gab da a haife su, amma ba ƙarfin da za a yi yunƙuri a haife su.
شاید یهوه خدایت تمامی سخنان ربشاقی را که آقایش، پادشاه آشور، او را برای اهانت نمودن خدای حی فرستاده است، بشنود و سخنانی را که یهوه، خدایت شنیده است، توبیخ نماید. پس برای بقیه‌ای که یافت می‌شوند، تضرع نما.» ۴ 4
Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun sarkin yaƙi, wanda maigidansa, sarkin Assuriya, ya aiko don yă rena Allah mai rai. Bari Ubangiji Allahnka yă tsawata masa saboda maganar da ya ji. Saboda haka ka yi addu’a domin raguwar da har yanzu suke a raye.”
وبندگان حزقیای پادشاه نزد اشعیا آمدند. ۵ 5
Da fadawan sarki Hezekiya suka isa wurin Ishaya,
و اشعیابه ایشان گفت: «به آقای خود چنین گویید که خداوند چنین می‌فرماید: از سخنانی که شنیدی که بندگان پادشاه آشور به آنها به من کفرگفته‌اند، مترس. ۶ 6
Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku, in ji Ubangiji, ‘Kada abin da ka ji yă firgita ka, wato, waɗannan kalmomin da karen nan na sarkin Assuriya ya yi saɓo da su.
همانا روحی بر او می‌فرستم که خبری شنیده، به ولایت خود خواهد برگشت و اورا در ولایت خودش به شمشیر هلاک خواهم ساخت.» ۷ 7
Saurara! Zan sa masa wani ruhun da zai sa yă ji wata jita-jitar da za tă sa yă koma ƙasarsa. A can zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’”
پس ربشاقی مراجعت کرده، پادشاه آشور را یافت که با لبنه جنگ می‌کرد، زیرا شنیده بود که ازلاکیش کوچ کرده است. ۸ 8
Da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye, ya kuma iske sarkin yana yaƙi da Libna.
و درباره ترهاقه، پادشاه حبش، خبری شنیده بود که به جهت مقاتله با توبیرون آمده است (پس چون شنید) بار دیگرایلچیان نزد حزقیا فرستاده، گفت: ۹ 9
To, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana zuwa masa da yaƙi. Saboda haka ya sāke aika manzanni zuwa wurin Hezekiya cewa,
«به حزقیا، پادشاه یهودا چنین گویید: «خدای تو که به اوتوکل می‌نمایی، تو را فریب ندهد و نگوید که اورشلیم به‌دست پادشاه آشور تسلیم نخواهدشد. ۱۰ 10
“Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda, kada ka bar allahn da kake dogara gare shi yă ruɗe ka cewa, ‘Urushalima ba za tă fāɗi a hannun sarkin Assuriya ba.’
اینک تو شنیده‌ای که پادشاهان آشور باهمه ولایتها چه کرده و چگونه آنها را بالکل هلاک ساخته‌اند، و آیا تو رهایی خواهی یافت؟ ۱۱ 11
Ba shakka ka riga ka ji abin da sarkin Assuriya ya yi da dukan ƙasashe, yana hallaka su gaba ɗaya. Kai kuwa kana ji za a cece ka?
آیا خدایان امتهایی که پدران من، ایشان راهلاک ساختند، مثل جوزان و حاران و رصف وبنی عدن که در تلسار می‌باشند، ایشان را نجات دادند؟ ۱۲ 12
Allolin al’umman da kakannina suka hallaka, sun cece su ne, allolin Gozan, da na Haran, da na Rezef, da kuma na mutane Eden da suke a Tel Assar?
پادشاه حمات کجاست؟ و پادشاه ارفاد و پادشاه شهر سفروایم و هینع و عوا؟» ۱۳ 13
Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin birnin Sefarfayim, ko na Hena da kuma na Iffa?”
و حزقیا مکتوب را از دست ایلچیان گرفته، آن را خواند و حزقیا به خانه خداوند درآمده، آن را به حضور خداوند پهن کرد. ۱۴ 14
Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga manzannin ya karanta. Sa’an nan ya tashi ya tafi haikalin Ubangiji ya shimfiɗa wasiƙar a gaban Ubangiji.
و حزقیا نزدخداوند دعا نموده، گفت: «ای یهوه، خدای اسرائیل که بر کروبیان جلوس می‌نمایی، تویی که به تنهایی بر تمامی ممالک جهان خدا هستی و توآسمان و زمین را آفریده‌ای. ۱۵ 15
Hezekiya kuwa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda yake zaune tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah bisa dukan mulkokin duniya. Kai ka yi sama da duniya.
‌ای خداوند گوش خود را فرا‌گرفته، بشنو. ای خداوند چشمان خودرا گشوده، ببین و سخنان سنحاریب را که به جهت اهانت نمودن خدای حی فرستاده است، استماع نما. ۱۶ 16
Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka ji; ka buɗe idanunka ya Ubangiji ka gani; ka saurari kalmomin da Sennakerib ya aiko don yă yi wa Allah mai rai ba’a.
‌ای خداوند، راست است که پادشاهان آشور امت‌ها و زمین ایشان را خراب کرده است، ۱۷ 17
“Da gaske ne, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriya sun hallakar da waɗannan al’ummai da ƙasashensu.
و خدایان ایشان را به آتش انداخته، زیرا که خدا نبودند، بلکه ساخته دست انسان از چوب وسنگ. پس به این سبب آنها را تباه ساختند. ۱۸ 18
Sun jefar da allolinsu cikin wuta, suka hallaka su, gama ba alloli ba ne, katakai ne da kuma duwatsu, ayyukan hannuwan mutane.
پس حال یهوه، خدای ما، ما را از دست اورهایی ده تا جمیع ممالک جهان بدانند که تو تنهاای یهوه، خدا هستی.» ۱۹ 19
To, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, don dukan mulkokin duniya su san cewa kai kaɗai, ya Ubangiji ne Allah.”
پس اشعیا ابن آموص نزد حزقیا فرستاده، گفت: «یهوه، خدای اسرائیل، چنین می‌گوید: آنچه را که درباره سنحاریب، پادشاه آشور، نزدمن دعا نمودی اجابت کردم. ۲۰ 20
Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo zuwa wurin Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, na ji addu’arka game da Sennakerib sarkin Assuriya.
کلامی که خداوند درباره‌اش گفته، این است: آن باکره، دختر صهیون، تو را حقیر شمرده، استهزا نموده است و دختر اورشلیم سر خود را به تو جنبانیده است. ۲۱ 21
Ga abin da Ubangiji yana cewa game da shi, “‘Budurwar Sihiyona ta rena ka tana kuma yin maka ba’a. Diyar Urushalima ta kaɗa kanta yayinda kake gudu.
کیست که او را اهانت کرده، کفر گفته‌ای و کیست که بر وی آواز بلند کرده، چشمان خودرا به علیین افراشته‌ای؟ مگر قدوس اسرائیل نیست؟ ۲۲ 22
Wane ne ka zaga, ka kuma yi masa saɓo? Wa kake gāba da shi har ka ɗaga muryarka, har ka tā da idanunka da fahariya? Kana gāba da Mai Tsarki na Isra’ila!
به واسطه رسولانت، خداوند را اهانت کرده، گفته‌ای: به کثرت ارابه های خود بر بلندی کوهها و به اطراف لبنان برآمده‌ام و بلندترین سروهای آزادش و بهترین صنوبرهایش را قطع نموده، به بلندی اقصایش و به درختستان بوستانش داخل شده‌ام. ۲۳ 23
Ta wurin manzanninka ka tara wa Ubangiji zagi. Ka kuma ce, “Da yawa kekunan yaƙina na haye kan ƙwanƙolin duwatsu, wurin mafi tsawo na Lebanon. Na sassare itacen al’ul nasa mafi tsawo mafi daraja na itacen fir nasa. Na ratsa har can tsakiyar kurmi, mafi kyau na kurminsa.
و من، حفره کنده، آب غریب نوشیدم و به کف پای خود تمامی نهرهای مصر را خشک خواهم کرد. ۲۴ 24
Na tona rijiyoyi a ƙasashen waje na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.”
آیا نشنیده‌ای که من این را از زمان سلف کرده‌ام و از ایام قدیم صورت داده‌ام و الان، آن را به وقوع آورده‌ام تا توبه ظهور آمده و شهرهایی حصاردار را خراب نموده، به توده های ویران مبدل سازی؟ ۲۵ 25
“‘Ba ka taɓa ji ba? Tun da daɗewa na ƙaddara haka. Tuntuni kuwa na shirya shi; yanzu kuma na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu katanga tarin duwatsu.
از این جهت، ساکنان آنها کم قوت بوده، ترسان و خجل شدند، مثل علف صحرا و گیاه سبز و علف پشت بام و مثل غله‌ای که پیش از رسیدنش پژمرده شود، گردیدند. ۲۶ 26
Ƙarfin mutanensu ya tsiyaye, suka razana aka kuma kunyata su. Suna kama da tsirai a gona, kamar sabon toho kamar ciyawa mai tohuwa bisa rufin ɗaki wanda ya bushe saboda zafi, kafin yă yi girma.
«اما من نشستن تو را و خروج و دخولت وخشمی را که بر من داری، می‌دانم. ۲۷ 27
“‘Amma na san wurin zamanka da fitarka da shigarka da yadda kake fushi da ni.
چونکه خشمی که بر من داری و غرور تو، به گوش من برآمده است. بنابراین مهار خود را به بینی تو ولگام خود را به لبهایت گذاشته، تو را به راهی که آمده‌ای، برخواهم گردانید. ۲۸ 28
Domin kana fushi da ni reninka ya iso kunnuwata, zan sa ƙugiyata a hancinka da linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma a ta hanyar da ka zo.’
«و علامت، برای تو این خواهد بود که امسال غله خودرو خواهید خورد و سال دوم آنچه از آن بروید و در سال سوم بکارید و بدرویدو تاکستانها غرس نموده، میوه آنها را بخورید. ۲۹ 29
“Wannan zai zama alama a gare ka, ya Hezekiya, “Bana, za ku ci amfanin gonar da ya tsira da kansa, baɗi kuma amfanin gonar da ya tsiro daga na bara. Amma a shekara ta uku, za ku yi shuki, ku kuma girbe, ku dasa gonakin inabi, ku kuma ci’ya’yansa.
و بقیه‌ای که از خاندان یهودا رستگار شوند، باردیگر به پایین ریشه خواهند زد و به بالا میوه خواهند‌آورد. ۳۰ 30
Sau ɗaya kuma ragowar masarautar Yahuda za tă yi saiwoyi a ƙasa ta kuma ba da’ya’ya a bisa.
زیرا که بقیه‌ای از اورشلیم ورستگاران از کوه صهیون بیرون خواهند آمد. غیرت یهوه این را بجا خواهد آورد. ۳۱ 31
Gama daga Urushalima za a sami ragowa, daga Dutsen Sihiyona kuma za a sami waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki za tă cika wannan.
«بنابراین خداوند درباره پادشاه آشورچنین می‌گوید که «به این شهر داخل نخواهد شدو به اینجا تیر نخواهد انداخت و در مقابلش با سپرنخواهد آمد و منجنیق را در‌پیش آن بر نخواهدافراشت. ۳۲ 32
“Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga birnin nan ba ko yă harba kibiya a nan. Ba zai kusace ta da garkuwa ko yă yi mata zoben yaƙi ba.
به راهی که آمده است به همان برخواهد گشت و به این شهر داخل نخواهد شد. خداوند این را می‌گوید. ۳۳ 33
Ta hanyar da ya zo ne zai koma; ba zai shiga birnin nan ba, in ji Ubangiji.
زیرا که این شهر راحمایت کرده، به‌خاطر خود و به‌خاطر بنده خویش داود، آن را نجات خواهم داد.» ۳۴ 34
Zan kāre birnin nan in cece ta, saboda kaina da kuma bawana Dawuda.”
پس فرشته خداوند در آن شب بیرون آمده، صد و هشتاد و پنج هزار نفر از اردوی آشور را زدو بامدادان چون برخاستند، اینک جمیع آنهالاشه های مرده بودند. ۳۵ 35
A daren nan mala’ikan Ubangiji ya fita ya kashe dakaru dubu ɗari da tamanin da biyu a sansanin Assuriyawa. Da mutane suka farka da safe, sai ga gawawwaki ko’ina.
و سنحاریب، پادشاه آشور کوچ کرده، روانه گردید و برگشته، درنینوی ساکن شد. ۳۶ 36
Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya tā da sansanin ya kuma janye. Ya koma Ninebe ya zauna a can.
و واقع شد که چون او درخانه خدای خویش، نسروک عبادت می‌کرد، پسرانش ادرملک و شرآصر او را به شمشیر زدند، و ایشان به زمین آرارات فرار کردند و پسرش آسرحدون به‌جایش سلطنت نمود. ۳۷ 37
Wata rana yayinda yake sujada a haikalin Nisrok, allahnsa, sai’ya’yansa maza, Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka gudu zuwa ƙasar Ararat. Sai Esar-Haddon ɗansa ya gāje shi.

< دوم پادشاهان 19 >