< دوم تواریخ 7 >

و چون سلیمان از دعا کردن فارغ شد، آتش از آسمان فرود آمده، قربانی های سوختنی و ذبایح را سوزانید و جلال خداوند خانه را مملوساخت. ۱ 1
Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
و کاهنان به خانه خداوند نتوانستندداخل شوند، زیرا جلال یهوه خانه خداوند را پرکرده بود. ۲ 2
Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
و چون تمامی بنی‌اسرائیل آتش را که فرود می‌آمد و جلال خداوند را که بر خانه می‌بوددیدند، روی خود را به زمین بر سنگفرش نهادند وسجده نموده، خداوند را حمد گفتند که او نیکواست، زیرا که رحمت او تا ابدالاباد است. ۳ 3
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
و پادشاه و تمامی قوم قربانی‌ها در حضورخداوند گذرانیدند. ۴ 4
Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
و سلیمان پادشاه بیست ودو هزار گاو و صد و بیست هزار گوسفند برای قربانی گذرانید و پادشاه و تمامی قوم، خانه خدا را تبریک نمودند. ۵ 5
Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
و کاهنان بر سر شغلهای مخصوص خود ایستاده بودند و لاویان، آلات نغمه خداوند را (به‌دست گرفتند) که داود پادشاه آنها را ساخته بود، تا خداوند را به آنها حمدگویند، زیرا که رحمت او تا ابدالاباد است، و داودبه وساطت آنها تسبیح می‌خواند و کاهنان پیش ایشان کرنا می‌نواختند و تمام اسرائیل ایستاده بودند. ۶ 6
Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
و سلیمان وسط صحنی را که پیش خانه خداوند بود، تقدیس نمود زیرا که در آنجاقربانی های سوختنی و پیه ذبایح سلامتی رامی گذرانید، چونکه مذبح برنجینی که سلیمان ساخته بود، قربانی های سوختنی وهدایای آردی و پیه ذبایح را گنجایش نداشت. ۷ 7
Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
و در آنوقت سلیمان و تمامی اسرائیل با وی هفت روز را عید نگاه داشتند و آن انجمن بسیاربزرگ از مدخل حمات تا نهر مصر بود. ۸ 8
Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
و درروز هشتم محفلی مقدس برپا داشتند، زیرا که برای تبریک مذبح هفت روز و برای عید هفت روز نگاه داشتند. ۹ 9
A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
و در روز بیست و سوم ماه هفتم قوم را به خیمه های ایشان مرخص فرمود وایشان به‌سبب احسانی که خداوند به داود وسلیمان و قوم خود اسرائیل کرده بود، شادمان وخوشدل بودند. ۱۰ 10
A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
پس سلیمان خانه خداوند و خانه پادشاه راتمام کرد و هرآنچه سلیمان قصد نموده بود که درخانه خداوند و در خانه خود بسازد، آن را نیکو به انجام رسانید. ۱۱ 11
Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
و خداوند بر سلیمان در شب ظاهر شده، اورا گفت: «دعای تو را اجابت نمودم و این مکان رابرای خود برگزیدم تا خانه قربانی‌ها شود. ۱۲ 12
sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
اگرآسمان را ببندم تا باران نبارد و اگر امر کنم که ملخ، حاصل زمین را بخورد و اگر وبا در میان قوم خودبفرستم، ۱۳ 13
“Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
و قوم من که به اسم من نامیده شده اندمتواضع شوند، و دعا کرده، طالب حضور من باشند، و از راههای بد خویش بازگشت نمایند، آنگاه من از آسمان اجابت خواهم فرمود، وگناهان ایشان را خواهم آمرزید و زمین ایشان راشفا خواهم داد. ۱۴ 14
in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
و از این به بعد چشمان من گشاده، و گوشهای من به دعایی که در این مکان کرده شود شنوا خواهد بود. ۱۵ 15
Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
و حال این خانه رااختیار کرده، و تقدیس نموده‌ام که اسم من تا به ابددر آن قرار گیرد و چشم و دل من همیشه بر آن باشد. ۱۶ 16
Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
و اگر تو به حضور من سلوک نمایی، چنانکه پدرت داود سلوک نمود و برحسب هرآنچه تو را امر فرمایم عمل نمایی و فرایض واحکام مرا نگاه داری، ۱۷ 17
“Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
آنگاه کرسی سلطنت تورا استوار خواهم ساخت چنانکه با پدرت داودعهد بسته، گفتم کسی‌که بر اسرائیل سلطنت نماید از تو منقطع نخواهد شد. ۱۸ 18
zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
«لیکن اگر شما برگردید و فرایض و احکام مرا که پیش روی شما نهاده‌ام ترک نمایید و رفته، خدایان غیر را عبادت کنید، و آنها را سجده نمایید، ۱۹ 19
“Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
آنگاه ایشان را از زمینی که به ایشان داده‌ام خواهم کند و این خانه را که برای اسم خودتقدیس نموده‌ام، از حضور خود خواهم افکند وآن را در میان جمیع قوم‌ها ضرب‌المثل و مسخره خواهم ساخت. ۲۰ 20
zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
و این خانه که اینقدر رفیع است هرکه از آن بگذرد متحیر شده، خواهدگفت: برای چه خداوند به این زمین و به این خانه چنین عمل نموده است؟ ۲۱ 21
Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
و جواب خواهندداد: چونکه یهوه خدای پدران خود را که ایشان رااز زمین مصر بیرون آورد ترک کردند و به خدایان غیر متمسک شده، آنها را سجده و عبادت نمودند از این جهت تمامی این بلا را بر ایشان وارد آورده است.» ۲۲ 22
Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”

< دوم تواریخ 7 >