< اول پادشاهان 9 >

و واقع شد که چون سلیمان از بنا نمودن خانه خداوند و خانه پادشاه و از بجا آوردن هر مقصودی که سلیمان خواسته بود، فارغ شد، ۱ 1
Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
خداوند بار دیگر به سلیمان ظاهر شد، چنانکه در جبعون بر وی ظاهر شده بود. ۲ 2
sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
و خداوند وی را گفت: «دعا و تضرع تو را که به حضور من کردی، اجابت نمودم، و این خانه‌ای را که بنانمودی تا نام من در آن تا به ابد نهاده شود تقدیس نمودم، و چشمان و دل من همیشه اوقات در آن خواهد بود. ۳ 3
Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
پس اگر تو با دل کامل و استقامت به طوری که پدرت داود رفتار نمود به حضور من سلوک نمایی، و هر‌چه تو را امر فرمایم بجا آوری و فرایض و احکام مرا نگاه داری، ۴ 4
“Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
آنگاه کرسی سلطنت تو را بر اسرائیل تا به ابد برقرار خواهم گردانید، چنانکه به پدر تو داود وعده دادم و گفتم که از تو کسی‌که بر کرسی اسرائیل بنشیند، مفقودنخواهد شد. ۵ 5
zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
«اما اگر شما و پسران شما از متابعت من روگردانیده، اوامر و فرایضی را که به پدران شمادادم نگاه ندارید و رفته، خدایان دیگر را عبادت نموده، آنها را سجده کنید، ۶ 6
“Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
آنگاه اسرائیل را ازروی زمینی که به ایشان دادم منقطع خواهم ساخت، و این خانه را که به جهت اسم خودتقدیس نمودم از حضور خویش دور خواهم‌انداخت، و اسرائیل در میان جمیع قومهاضرب‌المثل و مضحکه خواهد شد. ۷ 7
sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
و این خانه عبرتی خواهد گردید به طوری که هر‌که نزد آن بگذرد، متحیر شده، صفیر خواهد زد و خواهندگفت: خداوند به این زمین و به این خانه چرا چنین عمل نموده است؟ ۸ 8
Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
و خواهند گفت: از این جهت که یهوه، خدای خود را که پدران ایشان را از زمین مصر بیرون آورده بود، ترک کردند و به خدایان دیگر متمسک شده، آنها را سجده و عبادت نمودند. لهذا خداوند تمامی این بلا را بر ایشان آورده است.» ۹ 9
Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
و واقع شد بعد از انقضای بیست سالی که سلیمان این دو خانه، یعنی خانه خداوند و خانه پادشاه را بنا می‌کرد، ۱۰ 10
A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
و حیرام، پادشاه صور، سلیمان را به چوب سرو آزاد و چوب صنوبر وطلا موافق هر‌چه خواسته بود اعانت کرده بود، آنگاه سلیمان پادشاه بیست شهر در زمین جلیل به حیرام داد. ۱۱ 11
sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
و حیرام به جهت دیدن شهرهایی که سلیمان به او داده بود، از صور بیرون آمد اماآنها به نظرش پسند نیامد. ۱۲ 12
Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
و گفت: «ای برادرم این شهرهایی که به من بخشیده‌ای چیست؟» وآنها را تا امروز زمین کابول نامید. ۱۳ 13
Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
و حیرام صد و بیست وزنه طلا برای پادشاه فرستاد. ۱۴ 14
Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
و این است حساب سخره‌ای که سلیمان پادشاه گرفته بود به جهت بنای خانه خداوند وخانه خود و ملو و حصارهای اورشلیم و حاصورو مجدو و جازر. ۱۵ 15
Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
زیرا که فرعون، پادشاه مصربرآمده، جازر را تسخیر نموده، و آن را به آتش سوزانیده، و کنعانیان را که در شهر ساکن بودندکشته بود، و آن را به دختر خود که زن سلیمان بودبه جهت مهر داده بود. ۱۶ 16
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
و سلیمان، جازر وبیت حورون تحتانی را بنا کرد. ۱۷ 17
Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
و بعلت و تدمررا در صحرای زمین، ۱۸ 18
da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
و جمیع شهرهای مخزنی که سلیمان داشت و شهرهای ارابه‌ها وشهرهای سواران را و هر‌آنچه را که سلیمان میل داشت که در اورشلیم و لبنان و تمامی زمین مملکت خود بنا نماید (بنا نمود). ۱۹ 19
Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
و تمامی مردمانی که از اموریان و حتیان و فرزیان و حویان و یبوسیان باقی‌مانده، و از بنی‌اسرائیل نبودند، ۲۰ 20
Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
یعنی پسران ایشان که در زمین باقی ماندند بعداز آنانی که بنی‌اسرائیل نتوانستند ایشان را بالکل هلاک سازند، سلیمان ایشان را تا امروزخراج گذار و غلامان ساخت. ۲۱ 21
wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
اما ازبنی‌اسرائیل، سلیمان احدی را به غلامی نگرفت، بلکه ایشان مردان جنگی و خدام و سروران وسرداران و روسای ارابه‌ها و سواران او بودند. ۲۲ 22
Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
و اینانند ناظران خاصه که بر کارهای سلیمان بودند، پانصد و پنجاه نفر که بر اشخاصی که در کار مشغول می‌بودند، سرکاری داشتند. ۲۳ 23
Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
پس دختر فرعون از شهر داود به خانه خودکه برایش بنا کرده بود، برآمد، و در آن زمان ملو رابنا می‌کرد. ۲۴ 24
Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
و سلیمان هر سال سه مرتبه قربانی های سوختنی و ذبایح سلامتی بر مذبحی که به جهت خداوند بنا کرده بود می‌گذرانید، و بر مذبحی که پیش خداوند بود، بخور می‌گذرانید. پس خانه رابه اتمام رسانید. ۲۵ 25
Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
و سلیمان پادشاه در عصیون جابر که به‌جانب ایلوت بر کناره بحر قلزم در زمین ادوم است، کشتیها ساخت. ۲۶ 26
Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
و حیرام، بندگان خود راکه ملاح بودند و در دریا مهارت داشتند، درکشتیها همراه بندگان سلیمان فرستاد. ۲۷ 27
Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
پس به اوفیر رفتند و چهارصد و بیست وزنه طلا از آنجاگرفته، برای سلیمان پادشاه آوردند. ۲۸ 28
Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.

< اول پادشاهان 9 >