< Salmenes 59 >
1 Til songmeisteren; «tyn ikkje»; av David; ein miktam, då Saul sende folk som gjætte på huset og vilde drepa honom. Frels meg frå mine fiendar, min Gud, berga meg frå deim som stend upp imot meg!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Frels meg frå deim som gjer urett, og berga meg frå blodgiruge menner!
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 For sjå, dei ligg på lur etter mi sjæl, sterke menner slær seg saman imot meg, Herre, utan mi misgjerd og utan mi synd.
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 Utan mi skuld renner dei fram og gjer seg ferdige. Vakna og møt meg, og sjå!
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 Ja du, Herre, allhers drott, Israels Gud, vakna til å heimsøkja alle heidningar, ver ikkje nådig mot nokon av dei falske nidingar! (Sela)
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 Dei kjem att um kvelden, dei hyler som hundar og renner kring i byen.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 Sjå, dei let det gøysa ut or munnen sin, der er sverd i deira lippor, for: «Kven høyrer?»
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 Men du, Herre, lær åt deim, du spottar alle heidningar.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 Mot hans magt vil eg venta på deg, for Gud er mi borg.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 Min Gud vil møta meg med si nåde, Gud vil lata meg sjå med lyst på deim som lurer på meg.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 Drep deim ikkje, at ikkje mitt folk skal gløyma det! Driv deim ikring ved di magt og støyt deim ned, du Herre, vår skjold!
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 Kvart ord på deira lippor er ei synd i deira munn; lat deim so verta fanga i sitt ovmod og for den banning og lygn som dei talar!
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 Gjer ende på deim i vreide, gjer ende på deim, so dei ikkje meir er til, og lat dei vita at Gud er Herre i Jakob, alt til endarne av jordi! (Sela)
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 Og dei kjem att um kvelden, hyler som hundar og renner kring i byen.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 Dei flakkar um etter mat, vert dei ikkje mette, nattar dei yver.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 Men eg vil syngja um di magt og um morgonen lovsyngja di miskunn; for du er mi borg og mi livd den dag eg er i naud.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 Min styrke! for deg vil eg syngja; for Gud er mi borg, min miskunnsame Gud.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.