< Salmenes 29 >
1 Ein salme av David. Gjev Herren, de Guds søner, gjev Herren æra og magt!
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Gjev Herren hans namns æra, tilbed Herren i heilag prydnad!
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 Herrens røyst ljodar yver vatni, Gud den herlege torar, Herren yver dei store vatn.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 Herrens røyst ljodar med velde, Herrens røyst med herlegdom.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 Herrens røyst bryt sund cedertre, ja, Herren bryt sund cedertrei på Libanon.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 Og han fær deim til å hoppa som ein kalv, Libanon og Sirjon som ein ung villukse.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 Herrens røyst sprengjer eldslogar fram.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 Herrens røyst fær øydemarki til å skjelva, Herren fær øydemarki ved Kades til å skjelva.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 Herrens røyst fær hindarne til å kalva og snøyder skogarne, og i hans tempel segjer alt: «Æra!»
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Herren sat yver storflodi, og Herren sit konge til æveleg tid.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Herren gjeve sitt folk styrke, Herren velsigne sitt folk med fred!
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.