< Mika 6 >
1 Høyr kva Herren segjer: Reis deg! Før di sak for fjelli! Lat haugarne høyra di røyst!
Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
2 Ja, høyr Herrens sak, de fjell og de ævelege grunnvollar under jordi! For Herren fører sak med folket sitt, og med Israel vil han ganga til doms.
“Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
3 Mitt folk, kva hev eg gjort deg? Kva hev eg trøytta deg med? Svara meg!
“Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
4 Eg førde deg då ut or Egyptarlandet, og frå trælehuset løyste eg deg ut; og Moses og Aron og Mirjam sette eg i brodden for deg.
Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
5 Mitt folk! Kom i hug det Balak, kongen i Moab, var meint på, og det Bileam Beorsson svara honom! Kom i hug ferdi frå Sittim til Gilgal, so du kann skyna Herrens rettferdsverk!
Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
6 Kva skal eg stiga fram for Herren med, bøygja meg med for Gud i det høge? Skal eg stiga fram for honom med brennoffer, med årsgamle kalvar?
Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
7 Vil Herren hava hugnad i tusund verar, i ti tusund oljebekkjer? Skal eg ofra min fyrstefødde for mitt brot, mi livsfrukt til syndoffer for mi sjæl?
Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
8 Nei, han hev sagt deg, menneskje, kva som godt er; for kva krev Herren av deg anna enn at du skal gjera det som rett er, leggja vinn på kjærleik og ferdast audmjukt med din Gud?
Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
9 Høyr kor Herren ropar til byen - og det er visdom å ottast namnet ditt -. Høyr straffi, og kven det er som hev fastsett henne!
Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
10 Finst det endå i huset åt den gudlause rangfenge skattar og undermåls skjeppemål, som er bannstøytt?
Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
11 Kunde eg vera rein dersom eg bruka svikefulle vegtar og hadde falske lodd i pungen?
Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
12 Du by med rikfolk, fulle av urett, og dei som bur der, talar lygn og hev ei falsk tunga i munnen sin!
Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
13 So vil då eg og slå deg so det gjer vondt, leggja deg i øyde for dine synder skuld.
Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
14 Du skal eta, men ikkje verta mett, og tom skal du alltid kjenna deg. Du kann flytja, men du skal ikkje berga. Og det du bergar, skal eg gjeva åt sverdet.
Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
15 Du skal så, men ikkje få hausta. Du skal pressa olivor, men ikkje få salva deg med olje. Du skal pressa druvesaft, men ikkje få drikka vin.
Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
16 For fyreskrifterne åt Omri agtar dei vel på, og all gjerning av Ahabs hus, og etter deira råder er det de ferdast, for eg skal gjera deg til ei skræma og ibuarane dine til spott, og vanæra yver folket mitt skal de bera.
Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”