< Jobs 37 >

1 For dette bivrar hjarta mitt og lyfter seg frå staden sin.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Å, høyr på harmen i hans røyst, den dun som dundrar or hans munn!
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Det fer burt under himmelkvelv, men elden skin til heimsens endar.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 So burar røysti etterpå, han torar med sitt stolte mod, og ljoni held han ikkje att når røysti si han ljoma let.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Gud torar underfullt med røysti, gjer storverk som me ei kann skyna.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Han snøen byd: «Fall ned til jord!» Til regnet og, sitt sterke silregn.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Han stengjer av for mannehand, so all hans skapning læra må.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Villdyri gjeng til sine hi og kvilar på sin legestad.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Or inste kammer kjem det storm, og kulde ut av vindarne.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Utav Guds ande gustar frost, dei vide vatni kjem i tvang.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Han lastar skyi og med væta og breider sine elding-skyer,
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 og hit og dit dei hastar fram, og skifter leid som han det vil og set i verk det som han byd, utyver vide jordheims-kringen;
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 anten til ris, når jordi treng det, ell’ og med nåde lyt dei råka.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Job, lyd på dette, statt no still, gjev gaum på undri Gud hev gjort!
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Veit du når Gud deim segjer fyre, og let sitt ljos or skyi skina?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Veit du vel korleis skyi sviv, um underi åt den Allvise?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Du som i heite klæde styn, når jordi brenn i sunnanvind?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Gjer du med honom himmelkvelven, som er so fast som støypte spegel?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Lær oss, kva me skal segja honom! Me tegja lyt for berre myrker.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Skal han få melding at eg talar? Vil nokon ynskja seg å tynast?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 No kann ein ikkje ljoset sjå, um enn det klårt på himmeln skin, men vinden sopar skyi burt.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Langt nordanfrå kjem gullet hit, ein fælsleg glans ligg yver Gud.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 Til Allvald kann me ikkje nå, til han som er so stor i magt; men rett og rettferd ei han krenkjer.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Difor ber folket age for han, han ansar ingen sjølvklok mann.»
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Jobs 37 >