< Jakobs 1 >

1 Jakob, Guds og Herren Jesu Kristi tenar, helsar dei tolv ætterne som er spreidde i framande land.
Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
2 Haldt det for berre gleda, mine brør, når de kjem ut i ymse freistingar,
Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
3 etter di de veit at prøvingi av dykkar tru verkar tolmod!
domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
4 Men tolmodet må føra til fullkome verk, so de kann vera fullkomne og heile og ikkje vanta noko.
Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
5 Men dersom nokon av dykk vantar visdom, so bede han Gud, han som gjev alle viljugt og utan vondord, og han skal få.
In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
6 Men han må beda med tru og ikkje tvilande; for den som tvilar, er liksom havbåra, som vert rørd og rugga av vinden.
Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
7 For ikkje må det menneskjet tru at han skal få noko av Herren,
Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
8 slik ein tvihuga mann, ustød på alle sine vegar.
shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
9 Men den låge broren rose seg av sin høgleik,
Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
10 og den rike av sin lågleik; for han skal kverva burt som blomen på graset:
Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
11 Soli gjekk upp med sin hite og gjorde graset turt, og blomen på det fall av, og hans fagre åsyn vart øydelagd. Soleis skal og den rike visna på sine vegar.
Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
12 Sæl den mannen som held ut i freisting! for når han er prøvd, skal han få livsens kruna, som Gud hev lova deim som elskar honom.
Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
13 Ingen må segja når han vert freista: «Eg vert freista av Gud; » for Gud er ikkje freista av det vonde, og sjølv freistar han ingen.
Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
14 Men kvar ein vert freista når han vert dregen og lokka av si eigi lyst!
amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
15 sidan, når lysti vert med barn, ber ho synd; men når syndi er fullmogna, føder ho daude.
Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
16 Far ikkje vilt, mine kjære brør!
Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
17 All god gåva og all fullkomi gåva kjem ovantil frå faderen til ljosi, han som det ikkje er umbrøyte ved eller skiftande skugge.
Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
18 Etter sin vilje hev han født oss ved sannings ord, so me skulde vera ei fyrstegrøde av hans skapningar.
Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
19 Det veit de, kjære brør! Men kvart menneskje vere snar til å høyra, sein til å tala, sein til vreide,
’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
20 for ein manns vreide verkar ikkje det som er rett for Gud.
gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
21 Legg difor av all ureinskap og alt som er att av vondskap, og tak med spaklynde imot ordet som er innplanta i dykk, og som er megtigt til å frelsa sjælerne dykkar!
Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
22 Men vert slike som gjer etter ordet og ikkje berre høyrer det og dermed dårar dykk sjølve!
Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
23 For dersom nokon høyrer ordet og ikkje gjer etter det, då er han lik ein mann som skodar sitt naturlege andlit i ein spegel;
Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
24 han skoda seg sjølv og gjekk burt og gløymde straks korleis han såg ut.
bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
25 Men den som ser inn i fridomens fullkomne lov og held ved med det, so han ikkje vert ein gløymsam tilhøyrar, men ein som gjer gjerningi, han skal vera sæl i si gjerning.
Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
26 Dersom nokon meiner at han er ein gudsdyrkar, og ikkje tøymer tunga si, men dårar sitt eige hjarta, hans gudsdyrking er fåfengd.
In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
27 Ei rein og lytelaus gudsdyrking for Gud og Faderen er dette: å sjå til faderlause og enkjor i deira trengsla, å halda seg sjølv uflekka av verdi.
Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.

< Jakobs 1 >