< 2 Kongebok 21 >
1 Tolv år gamall var Manasse då han vart konge, fem og femti år rådde han i Jerusalem. Mor hans heitte Hefsiba.
Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
2 Han gjorde det som vondt var i Herrens augo, likt med dei avstyggjelege skikkarne hjå dei folki Herren hadde rudt ut for Israels-borni.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Han bygde upp att dei offerhaugarne som Hizkia, far hans, hadde lagt i øyde, og reiste altar for Ba’al og laga Astarte-bilæte, liksom Ahab, Israels-kongen, hadde gjort, og kasta seg ned for og tente heile himmelheren.
Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
4 Ja, han bygde altar i Herrens hus, der som Herren hadde sagt: «Til Jerusalem vil eg festa namnet mitt.»
Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
5 I båe tuni kring Herrens hus bygde han altar for heile himmelheren.
Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
6 Han vigde son sin i elden og for med spådom og trolldom, og tinga folk til å mana fram draugar og spåvette. Han gjorde mykje som var vondt i Herrens augo, og harma honom.
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
7 Astarte-bilætet som han hadde laga, sette han i det huset som Herren hadde sagt um til David og Salomo, son hans: «Til dette huset og til Jerusalem, som eg hev valt ut millom alle Israels ætter, vil eg festa namnet mitt i all æva.
Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Eg vil ikkje meir lata Israel flakka heimlaus burt frå landet eg gav federne deira. Berre dei gjer og heldt seg etter alle mine bod og etter heile lovi som Moses, tenaren min, gav deim!»
Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
9 Men dei lydde ikkje. Manasse forførde deim, so dei stelte seg verre enn dei folki Herren hadde øydt ut for Israels-borni.
Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 Då tala Herren ved tenarane sine, profetarne, soleis:
Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
11 «Av di Manasse, Juda-kongen, hev drive med desse avstyggjelege skikkarne, verre enn alt det amoritarne gjorde fyre hans tid, og forført med sine steingudar ogso Juda til å synda,
“Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
12 so segjer Herren, Israels Gud: «Sjå, eg sendar ulukka yver Jerusalem og Juda, so det skal ringja for båe øyro på alle som høyrer det.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
13 Eg spanar same mælesnori yver Jerusalem som yver Samaria, og nyttar same vegtloddet som yver Ahabs hus. Eg turkar burt Jerusalem, liksom ein turkar av eit fat og so snur det upp ned.
Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
14 Eg støyter ifrå meg deim som er att av arvluten min, og gjev deim i fiendevald, so dei vert til ran og til herfang for alle sine fiendar.
Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
15 Og det av di dei hev gjort det som vondt er i mine augo, og jamt harma meg frå den dagen federne deira drog ut or Egyptarland og til den dag i dag.»»
domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
16 Manasse let og skuldlaust blod renna, i so stor mengd at Jerusalem vart fyllt av det frå ende til annan, umfram den syndi at han forførde Juda til å gjera det som vondt var i Herrens augo.
Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
17 Det som elles er å fortelja um Manasse, um det han gjorde og um hans synd, det er uppskrive i krønikeboki åt Juda-kongarne.
Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
18 Manasse lagde seg til kvile hjå federne sine, og vart gravlagd i slottshagen, i Uzzas hage. Og Amon, son hans, vart konge i staden hans.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
19 Tvo og tjuge år gamall var Amon då han vart konge; tvo år rådde han i Jerusalem. Mor hans heitte Mesullemet Harusdotter, frå Jotba.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
20 Han gjorde det som vondt var i Herrens augo, liksom Manasse, far hans;
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
21 han fylgde i alt fotefari til far sin, og tente steingudarne som far hans hadde tent, og bad til deim.
Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
22 Han vende seg frå Herren, sin fedregud, og gjekk ikkje på Herrens veg.
Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
23 Amons hirdmenner samansvor seg og drap kongen i huset hans.
Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
24 Landsfolket slo i hel deim som hadde samansvore seg saman mot Amon, og tok Josia, son hans, til konge i staden hans.
Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
25 Det som elles er å fortelja um Amon, det han gjorde, det er uppskrive i krønikeboki åt Juda-kongarne.
Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
26 Han vart gravlagd i gravi i Uzzias hage. Josia, son hans, vart konge i staden hans.
Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.