< Romerne 6 >
1 Hvad skal vi da si? skal vi holde ved i synden, forat nåden kan bli dess større?
Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba da yin zunubi domin alheri yă haɓaka?
2 Langt derifra! vi som er avdød fra synden, hvorledes skulde vi ennu leve i den?
Sam, ko kaɗan! Mun mutu ga zunubi; ta yaya za mu ci gaba da rayuwa a cikinsa kuma?
3 Eller vet I ikke at alle vi som blev døpt til Kristus Jesus, blev døpt til hans død?
Ko ba ku sani ba cewa dukanmu da aka yi wa baftisma a cikin Kiristi Yesu an yi mana baftismar ne zuwa cikin mutuwarsa?
4 Vi blev altså begravet med ham ved dåpen til døden, forat likesom Kristus blev opreist fra de døde ved Faderens herlighet, så skal også vi vandre i et nytt levnet.
Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka tā da Kiristi daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa.
5 For er vi blitt forenet med ham ved likheten med hans død, så skal vi også bli det ved likheten med hans opstandelse,
In kuwa mun zama ɗaya tare da shi haka a cikin mutuwarsa, tabbatacce mu ma za mu zama ɗaya tare da shi cikin tashinsa daga matattu.
6 da vi jo vet dette at vårt gamle menneske blev korsfestet med ham forat synde-legemet skulde bli til intet, så vi ikke mere skal tjene synden;
Gama mun san cewa an gicciye halayenmu na dā tare da shi domin a kawar da jikin nan mai zunubi don kada mu ƙara zama bayi ga zunubi
7 for den som er død, er rettferdiggjort fra synden.
domin duk wanda ya mutu an’yantar da shi daga zunubi ke nan.
8 Men er vi død med Kristus, da tror vi at vi også skal leve med ham,
To, in mun mutu tare da Kiristi, mun gaskata cewa za mu rayu tare da shi kuma.
9 fordi vi vet at efterat Kristus er opstanden fra de døde, dør han ikke mere; døden har ikke mere nogen makt over ham;
Gama mun san cewa da yake an tā da Kiristi daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba; mutuwa ba ta da sauran iko a kansa.
10 for sin død, den døde han én gang for synden, men sitt liv, det lever han for Gud.
Mutuwar da ya yi, ya mutu ne sau ɗaya tak, saboda yă shafe zunubi, amma rayuwar da yake yi, yana yi ne cikin tarayya da Allah.
11 Således skal også I akte eder som døde for synden, men levende for Gud i Kristus Jesus.
Haka ku ma, ku ɗauke kanku matattu ne ga ikon zunubi amma rayayyu cikin tarayya da Allah cikin Kiristi Yesu.
12 La derfor ikke synden herske i eders dødelige legeme, så I lyder dets lyster;
Saboda haka kada ku bar zunubi yă mallaki jikin nan naku mai mutuwa yă sa ku zama masu biyayya ga mugayen sha’awace-sha’awacensa.
13 by heller ikke eders lemmer frem for synden som urettferdighets våben, men by eder frem for Gud som de som av døde er blitt levende, og eders lemmer som rettferdighets våben for Gud!
Kada ku miƙa gaɓoɓin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin mugunta, sai dai ku miƙa kanku ga Allah, a matsayin waɗanda aka fitar da su daga mutuwa zuwa rai; ku kuma miƙa gaɓoɓin jikinku gare shi a matsayin kayan aikin adalci.
14 For synden skal ikke herske over eder; I er jo ikke under loven, men under nåden.
Gama zunubi ba zai zama maigidanku ba, domin ba kwa ƙarƙashin doka, sai dai ƙarƙashin alheri.
15 Hvad da? skal vi synde, siden vi ikke er under loven, men under nåden? Langt derifra!
Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba yin zunubi domin ba ma ƙarƙashin doka sai dai ƙarƙashin alheri? Sam, ko kaɗan!
16 vet I ikke at når I byr eder frem for nogen som tjenere til lydighet, da er I også tjenere under den som I så lyder, enten det er under synden til død eller under lydigheten til rettferdighet?
Ba ku sani ba cewa sa’ad da kuka miƙa kanku ga wani don ku yi masa biyayya a matsayin bayi, ko ku bayi ne ga zunubi, wanda yake kai ga mutuwa, ko kuwa ga biyayya, wadda take kai ga adalci, ashe, ba kun zama bayi ga wannan da kuke yi wa biyayya ba ke nan?
17 Men Gud være takk at I vel har vært syndens tjenere, men nu av hjertet er blitt lydige mot den lærdomsform som I er blitt overgitt til!
Amma godiya ga Allah don ko da yake a dā ku bayi ne ga ikon zunubi, da dukan zuciyarku kun yi biyayya ga irin koyarwar da aka danƙa muku.
18 Men idet I er blitt frigjort fra synden, er I trådt i rettferdighetens tjeneste.
An’yanta ku daga zunubi, kun kuma zama bayi ga aikin adalci.
19 Jeg taler på menneskelig vis for eders kjøds skrøpelighets skyld. For likesom I bød eders lemmer frem som tjenere for urenheten og urettferdigheten til urettferdighet, således by nu eders lemmer frem som tjenere for rettferdigheten til helliggjørelse!
Ina magana ne kamar mutane saboda kun raunana a jikinku. Kamar yadda kuka saba miƙa gaɓoɓin jikinku a bautar abubuwan ƙazanta da mugun aiki a kan mugun aiki, saboda haka yanzu sai ku miƙa su bayi ga aikin adalci mai kai ga zaman tsarki.
20 For dengang da I var syndens tjenere, var I fri fra rettferdigheten.
Sa’ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci.
21 Hvad frukt hadde I da dengang? Slikt som I nu skammer eder over; for utgangen på det er døden.
Wace riba ce kuka samu a lokacin, daga abubuwan nan da yanzu suka zama muku abin kunya? Ƙarshen irin abubuwan nan dai, mutuwa ne!
22 Men nu, da I er frigjort fra synden og er trådt i Guds tjeneste, har I eders frukt til helliggjørelse, og til utgang et evig liv. (aiōnios )
Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios )
23 For den lønn som synden gir, er døden, men Guds nådegave er evig liv i Kristus Jesus, vår Herre. (aiōnios )
Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios )