< Romerne 10 >
1 Brødre! mitt hjertes ønske og min bønn til Gud for dem er at de må bli frelst.
'Yan'uwana, muradin zuciyata da dukkan addu'oi na ga Allah dominsu shine don su sami ceton.
2 For jeg gir dem det vidnesbyrd at de har nidkjærhet for Gud, men ikke med skjønnsomhet;
Domin na shaida game da su cewa suna da kwazo game da Allah, amma ba a kan sani ba.
3 for da de ikke kjente Guds rettferdighet og strevde efter å grunne sin egen rettferdighet, gav de sig ikke inn under Guds rettferdighet.
Don, ba su da sani akan adalcin Allah, suna kokarin tabbatar da adalcin kansu. Ba su bada kan su ga adalcin Allah ba.
4 For Kristus er lovens ende, til rettferdighet for hver den som tror.
Gama Almasihu shi ne cikar doka zuwa ga adalci ga dukkan wadanda suka gaskata.
5 For Moses skriver om rettferdigheten av loven: Det menneske som gjør disse ting, skal leve ved dem;
Musa kam ya rubuta game da adalci da zai samu ta shari'a: ''mutumin da ya aikata adalcin shari'a, zai rayu ta wurin wannan adalcin.''
6 men rettferdigheten av troen sier så: Si ikke i ditt hjerte: Hvem skal fare op til himmelen - det vil si: for å hente Kristus ned -?
Amma adalcin da ya zo ta wurin bangaskiya yace, ''Kada ku ce a zuciyarku, wa zai hau zuwa sama?''(don ya sauko da Almasihu kasa).
7 eller: Hvem skal fare ned i avgrunnen - det vil si: for å hente Kristus op fra de døde -? (Abyssos )
Kada ku ce, ''Wa zai gangara zuwa kasa?'' (Wato wa zai fito da Almasihu daga cikin matattu). (Abyssos )
8 Men hvad sier den? Ordet er dig nær, i din munn og i ditt hjerte; det er troens ord, det som vi forkynner,
Amma me yake cewa? “kalmar tana kusa da kai a cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka.” Wato kalmar bangaskiya, wadda muke shaidawa.
9 for dersom du med din munn bekjenner at Jesus er Herre, og i ditt hjerte tror at Gud opvakte ham fra de døde, da skal du bli frelst;
Don idan da bakinka, ka shaida Yesu Ubangiji ne, kuma ka gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tashe shi daga matattu, za ka sami ceto.
10 for med hjertet tror en til rettferdighet, og med munnen bekjenner en til frelse.
Don da zuciya ne mutum yake gaskatawa zuwa ga adalci, da kuma baki ne yake shaida zuwa ga ceto.
11 For Skriften sier: Hver den som tror på ham, skal ikke bli til skamme.
Don nassi na cewa, ''Duk wanda ya gaskata da shi ba zai ji kunya ba,''
12 Det er jo ingen forskjell på jøde og greker; de har alle den samme Herre, som er rik nok for alle som påkaller ham;
Gama ba bambanci tsakanin Bayahude da Ba'al'ume. Gama dukkansu Ubangijinsu daya ne, Shi mayalwaci ne ga dukkan wanda ya kira shi.
13 for hver den som påkaller Herrens navn, skal bli frelst.
Duk wanda ya kira sunan Ubangiji zai sami ceto.
14 Hvorledes kan de da påkalle den som de ikke tror på? og hvorledes kan de tro der de ikke har hørt? og hvorledes kan de høre uten at det er nogen som forkynner?
To ta yaya zasu kira ga wanda basu gaskata ba? Kuma ta yaya zasu gaskata ga wanda ba su taba jin labarinsa ba?
15 og hvorledes kan de forkynne uten at de blir utsendt? som skrevet er: Hvor fagre deres føtter er som forkynner fred, som bærer godt budskap!
Kuma ta yaya zasu ji in ba ayi masu wa'azi ba? Kuma ta yaya zasu yi wa'azin in ba an aike su ba? - Kamar yadda yake a rubuce, “Ina misalin kyau na kafafun wadanda ke shaida labarin farin ciki na abubuwa masu kyau!”
16 Men ikke alle var lydige mot evangeliet. For Esaias sier: Herre! hvem trodde vel det han hørte av oss?
Amma ba dukkansu ne suka ji bishara ba. Gama Ishaya ya ce, ''Ubangiji, wa ya gaskata da sakon?
17 Så kommer da troen av forkynnelsen, og forkynnelsen ved Kristi ord;
Saboda haka bangaskiya na zuwa ta wurin ji, jin kuwa daga maganar Almasihu.
18 men jeg sier: Har de da ikke fått høre? Jo til visse; deres røst gikk ut til all jorden, og deres ord til jorderikes ende.
Amma na ce, “ko basu ji ba ne? I, tabbas'' muryarsu ta kai dukkan duniya, kuma kalmominsu sun kai har karshen duniya.''
19 Men jeg sier: Kjente da Israel ikke til det? Først sier Moses: Jeg vil gjøre eder nidkjære på det som ikke er et folk; på et uforstandig folk vil jeg gjøre eder harme;
yau, na ce, ''Ko Isra'ila basu sani ba ne?'' Da farko Musa ya ce, “Zan sa kuyi fushi da kishi da abin da ba al'umma ba. Abin da nake nufi nan shine al'ummar da basu da fahinta, zan more su, in tayar maku da hankali.''
20 og Esaias våger sig til å si: Jeg blev funnet av dem som ikke søkte mig; jeg åpenbarte mig for dem som ikke spurte efter mig;
Amma Ishaya da karfin hali ya ce, ''Ga wadanda basu neme ni ba suka same ni. Na bayyana ga wadanda basu nemi ni ba.
21 men om Israel sier han: Hele dagen rakte jeg mine hender ut til et ulydig og gjenstridig folk.
''Amma ga Isra'ila kam ya ce, '' na mika hannu na ga masu rashin biyayya dukkan tsawon rana, domin su mutane ne masu taurin kai.''