< Romerne 1 >

1 Paulus, Jesu Kristi tjener, kalt til apostel, utkåret til å forkynne Guds evangelium,
Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
2 som han forut lovte ved sine profeter i hellige skrifter,
Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
3 om hans Sønn, som efter kjødet er kommet av Davids ætt,
game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
4 som efter hellighets ånd er godtgjort å være Guds veldige Sønn ved opstandelsen fra de døde, Jesus Kristus, vår Herre,
Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
5 ved hvem vi fikk nåde og apostelembede for å virke troens lydighet blandt alle hedningefolkene til hans navns ære,
Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
6 blandt hvilke også I er kalt til Jesus Kristus
Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
7 - til alle Guds elskede, kalte, hellige som er i Rom: Nåde være med eder og fred fra Gud vår Fader og den Herre Jesus Kristus!
Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
8 Først takker jeg min Gud ved Jesus Kristus for eder alle, fordi eders tro er navnkundig i hele verden.
Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
9 For Gud, som jeg tjener i min ånd i hans Sønns evangelium, er mitt vidne hvor uavlatelig jeg kommer eder i hu,
Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
10 idet jeg alltid i mine bønner beder om at jeg dog endelig engang ved Guds vilje må få lykke til å komme til eder.
cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
11 For jeg lenges efter å se eder, så jeg kunde la eder få del med mig i nogen åndelig nådegave, forat I kunde styrkes,
Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
12 det vil si at jeg hos eder kunde vederkveges sammen med eder ved den felles tro, eders og min.
wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
13 Og jeg vil ikke, brødre, at I skal være uvitende om at jeg ofte har satt mig fore å komme til eder - men jeg er blitt hindret inntil nu - forat jeg kunde ha nogen frukt også blandt eder likesom blandt de andre hedningefolk.
Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
14 Jeg står i gjeld både til grekere og til barbarer, både til vise og uvise;
Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
15 således er jeg for min del villig til å forkynne evangeliet også for eder i Rom.
Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
16 For jeg skammer mig ikke ved evangeliet; for det er en Guds kraft til frelse for hver den som tror, både for jøde først og så for greker;
Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
17 for i det åpenbares Guds rettferdighet av tro til tro, som skrevet er: Den rettferdige, ved tro skal han leve.
Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
18 For Guds vrede åpenbares fra himmelen over all ugudelighet og urettferdighet hos mennesker som holder sannheten nede i urettferdighet;
Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
19 for det som en kan vite om Gud, ligger åpent for dem, for Gud har åpenbaret dem det.
gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
20 For hans usynlige vesen, både hans evige kraft og hans guddommelighet, er synlig fra verdens skapelse av, idet det kjennes av hans gjerninger, forat de skal være uten undskyldning, (aïdios g126)
Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios g126)
21 fordi de, enda de kjente Gud, dog ikke æret eller takket ham som Gud, men blev dårlige i sine tanker, og deres uforstandige hjerte blev formørket.
Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
22 Mens de gjorde sig til av å være vise, blev de dårer,
Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
23 og byttet den uforgjengelige Guds herlighet bort mot et billede, en avbildning av et forgjengelig menneske og av fugler og av firføtte dyr og av krypdyr.
suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
24 Derfor overgav også Gud dem i deres hjerters lyster til urenhet, til å vanære sine legemer sig imellem,
Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
25 de som byttet Guds sannhet bort mot løgn og æret og dyrket skapningen fremfor skaperen, han som er velsignet i evighet. Amen. (aiōn g165)
Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 Derfor overgav Gud dem til skammelige lyster; for både deres kvinner forvendte den naturlige bruk til den unaturlige,
Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
27 og på samme vis forlot også mennene den naturlige bruk av kvinnen og brente i sin lyst efter hverandre, så at menn drev skjenselsverk med menn, og fikk på sig selv det vvederlag for sin forvillelse som rett var.
Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
28 Og likesom de ikke brydde sig om å eie Gud i kunnskap, så overgav Gud dem til et sinn som intet duer, så de gjorde det usømmelige:
Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
29 fulle av all urettferdighet, vanart, havesyke, ondskap; fulle av avind, mord, trette, svik, list;
Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
30 øretutere, baktalere, gudsforhatte, voldsmenn, overmodige, storskrytere, opfinnsomme til ondt; ulydige mot foreldre,
da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
31 uforstandige, upålitelige, ukjærlige, ubarmhjertige;
su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
32 slike som godt kjenner Guds dom at de som gjør sådant, fortjener døden, og dog ikke bare gjør det, men endog holder med dem som gjør det.
Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.

< Romerne 1 >