< Salmenes 88 >

1 En sang; en salme av Korahs barn; til sangmesteren; efter Mahalat leannot; en læresalme av Heman, esrahitten. Herre, min frelses Gud! Om dagen og om natten roper jeg for dig.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 La min bønn komme for ditt åsyn, bøi ditt øre til mitt klagerop!
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 For min sjel er mett av ulykker, og mitt liv er kommet nær til dødsriket. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 Jeg aktes like med dem som farer ned i hulen; jeg er som en mann uten kraft,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 frigitt som en av de døde, lik de ihjelslagne som ligger i graven, som du ikke mere kommer i hu, fordi de er skilt fra din hånd.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Du har lagt mig i dypenes hule, på mørke steder, i avgrunner.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Din vrede tynger på mig, og med alle dine bølger trenger du mig. (Sela)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Du har drevet mine kjenninger langt bort fra mig, du har gjort mig vederstyggelig for dem; jeg er stengt inne og kommer ikke ut.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mitt øie er vansmektet av elendighet; jeg har påkalt dig, Herre, hver dag, jeg har utbredt mine hender til dig.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Mon du gjør undergjerninger for de døde, eller mon dødninger står op og priser dig? (Sela)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Mon der fortelles i graven om din miskunnhet, i avgrunnen om din trofasthet?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Mon din undergjerning blir kjent i mørket, og din rettferdighet i glemselens land?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Men jeg roper til dig, Herre, og om morgenen kommer min bønn dig i møte.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Hvorfor, Herre, forkaster du min sjel? Hvorfor skjuler du ditt åsyn for mig?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Elendig er jeg og døende fra ungdommen av; jeg bærer dine redsler, jeg må fortvile.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Din vredes luer har gått over mig, dine redsler har tilintetgjort mig.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 De har omgitt mig som vann hele dagen, de har omringet mig alle sammen.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Du har drevet venn og næste langt bort fra mig; mine kjenninger er det mørke sted.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Salmenes 88 >