< Salmenes 83 >
1 En sang, en salme av Asaf. Gud, ti ikke! Vær ikke stille og hold dig ikke rolig, Gud!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 For se, dine fiender larmer, og de som hater dig, løfter hodet.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Mot ditt folk legger de med svik hemmelige råd, og de rådslår mot dem du verner.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 De sier: Kom og la oss utslette dem, så de ikke mere er et folk, og Israels navn skal ikke mere kommes i hu.
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 For de har av hjertet rådslått med hverandre; mot dig inngår de pakt,
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 Edoms telt og ismaelittene, Moab og hagarenene,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal og Ammon og Amalek, Filistea tillikemed innbyggerne av Tyrus.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Også Assur har gitt sig i lag med dem, de er blitt Lots barns arm. (Sela)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Gjør med dem som med Midian, som med Sisera, som med Jabin ved bekken Kison!
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 De blev ødelagt ved En-Dor, de blev til gjødsel for jorden.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 La det gå dem, deres ypperste menn, som Oreb og som Se'eb, og alle deres fyrster som Sebah og som Salmunna,
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 dem som sier: Vi vil ta oss Guds boliger til eie!
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Min Gud, gjør dem som en støvhvirvel, som agner for vinden!
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Som en ild som tender en skog, og som en lue som setter fjell i brand,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 således forfølge du dem med din storm og forferde du dem med ditt stormvær!
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Fyll deres åsyn med skam, så de søker ditt navn, Herre!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 La dem blues og forferdes til evig tid, la dem bli til skamme og gå under!
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Og la dem kjenne at du alene har navnet Herre, den Høieste over all jorden!
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.