< Salmenes 81 >

1 Til sangmesteren, efter Gittit; av Asaf. Juble for Gud, vår styrke, rop med glede for Jakobs Gud!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Stem i sang og la pauken lyde, den liflige citar tillikemed harpen!
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Støt i basun i måneden, ved fullmånen, på vår høitids dag!
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 For det er en lov for Israel, en rett for Jakobs Gud.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Han satte det til et vidnesbyrd i Josef da han drog ut gjennem Egyptens land. - Jeg hørte en røst som jeg ikke kjente:
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 Jeg fridde hans skulder fra byrden, hans hender slapp fri fra bærekurven.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 I nøden ropte du, og jeg fridde dig ut; jeg svarte dig, skjult i tordenskyen, jeg prøvde dig ved Meriba-vannene. (Sela)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Hør, mitt folk, og jeg vil vidne for dig! Israel, o, at du vilde høre mig:
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 Det skal ikke være nogen fremmed gud hos dig, og du skal ikke tilbede utlendingens gud.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Jeg er Herren din Gud, som førte dig op av Egyptens land; lukk din munn vidt op, at jeg kan fylle den!
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Men mitt folk hørte ikke min røst, og Israel vilde ikke lyde mig.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Så lot jeg dem fare i sitt hjertes hårdhet, forat de skulde vandre i sine egne onde råd.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 O, at mitt folk vilde høre mig, og at Israel vilde vandre på mine veier!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 Om en liten stund vilde jeg da ydmyke deres fiender og vende min hånd imot deres motstandere.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 De som hater Herren, skulde smigre for dem, og deres tid skulde vare evindelig.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Og han skulde fø dem med den beste hvete, og jeg skulde mette dig med honning fra klippen.
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Salmenes 81 >