< Salmenes 64 >

1 Til sangmesteren; en salme av David. Hør, Gud, min røst når jeg klager, bevar mitt liv for fiendens skremsel!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
2 Skjul mig for de ondes lønnlige råd, for illgjerningsmenns larmende hop,
Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
3 som hvesser sin tunge som et sverd, legger på buen sin pil, det bitre ord,
Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
4 for å skyte den uskyldige i lønndom; med ett skyter de ham og frykter ikke.
Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
5 De gjør sitt onde råd fast; de forteller hvorledes de vil legge skjulte snarer; de sier: Hvem ser dem?
Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
6 De uttenker ugjerninger: Vi er ferdige, tanken er uttenkt - og menneskenes tanker og hjerter er dype.
Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
7 Da skyter Gud dem; med ett kommer pilen; slaget har rammet dem.
Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
8 Og de blir nedstyrtet, deres tunge kommer over dem; alle de som ser på dem, ryster på hodet.
Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
9 Og alle mennesker frykter og forkynner Guds gjerning, og de forstår hans verk.
Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
10 Den rettferdige gleder sig i Herren og tar sin tilflukt til ham, og alle opriktige av hjertet priser sig lykkelige.
Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!

< Salmenes 64 >