< Salmenes 6 >
1 Til sangmesteren, med strengelek; efter Sjeminit; en salme av David. Herre, straff mig ikke i din vrede og tukt mig ikke i din harme!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Vær mig nådig, Herre! for jeg er bortvisnet. Helbred mig, Herre! for mine ben er forferdet,
Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
3 og min sjel er såre forferdet; og du, Herre, hvor lenge?
Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
4 Vend om, Herre, utfri min sjel, frels mig for din miskunnhets skyld!
Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
5 For i døden kommer ingen dig i hu; hvem vil prise dig i dødsriket? (Sheol )
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
6 Jeg er trett av mine sukk, jeg gjennembløter min seng hver natt; med mine tårer væter jeg mitt leie.
Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
7 Borttæret av sorg er mitt øie; det er eldet for alle mine fienders skyld.
Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
8 Vik fra mig, alle I som gjør urett! For Herren har hørt min gråts røst,
Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
9 Herren har hørt min inderlige begjæring, Herren tar imot min bønn.
Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
10 Alle mine fiender skal bli til skamme og såre forferdet; de skal vike tilbake, bli til skamme i et øieblikk.
Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.