< Salmenes 58 >
1 Til sangmesteren; "Forderv ikke"; av David; en gyllen sang. Mon I virkelig ved å tie taler hvad rettferdig er, dømmer hvad rett er, I menneskebarn?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 I hjertet arbeider I jo på misgjerninger, i landet veier I ut eders henders vold.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 De ugudelige er avveket fra mors fang av; de som taler løgn, farer vill fra mors liv.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Gift har de lik ormegift; de er som en døv slange, som stopper sitt øre til,
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 så den ikke hører på slangetemmernes røst, på ham som er kyndig i å besverge.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 Gud, slå deres tenner inn i deres munn, knus de unge løvers kinntenner, Herre!
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 La dem forgå som vann som rinner bort! Legger nogen sine piler i buen, da la dem bli som uten odd!
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 La dem være som en snegl, som opløses mens den går, som en kvinnes ufullbårne foster, som ikke har sett solen!
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Før eders gryter kjenner tornekvistene, skal han blåse dem bort enten de er friske eller i brand.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 Den rettferdige skal glede sig, fordi han ser hevn; han skal tvette sine føtter i den ugudeliges blod.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 Og menneskene skal si: Der er dog frukt for den rettferdige, det er dog en Gud som dømmer på jorden.
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”