< Salmenes 47 >

1 Til sangmesteren; av Korahs barn; en salme. Klapp i hender, alle folk, juble for Gud med fryderop.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 For Herren, den Høieste, er forferdelig, en stor konge over all jorden.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 Han legger folkeslag under oss og folkeferd under våre føtter.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 Han utvelger oss vår arvelodd, Jakobs, hans elskedes herlighet. (Sela)
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Gud fór op under jubelrop, Herren under basuners lyd.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Lovsyng Gud, lovsyng! Lovsyng vår konge, lovsyng!
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 For Gud er all jordens konge; syng en sang som gjør vis!
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Gud er konge over folkene, Gud har satt sig på sin hellige trone.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Folkenes fyrster samler sig med Abrahams Guds folk; for jordens skjold hører Gud til, han er såre ophøiet.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.

< Salmenes 47 >