< Salmenes 35 >

1 Av David. Trett, Herre, med dem som tretter med mig! Strid mot dem som strider mot mig!
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Grip skjold og verge og reis dig til hjelp for mig!
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Dra spydet frem og steng veien for mine forfølgere! Si til min sjel: Jeg er din frelse!
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 La dem blues og bli til skamme som står mig efter livet! La dem vike tilbake med skam som tenker ondt imot mig!
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 La dem bli som agner for vinden, og Herrens engel støte dem bort!
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 La deres vei bli mørk og glatt, og Herrens engel forfølge dem!
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 For uten årsak har de lønnlig gjort i stand sin garngrav for mig, uten årsak har de gravd en grav for mitt liv.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 La ødeleggelse komme over ham, uten at han merker det, og la hans garn som han lønnlig har utlagt, fange ham, la ham falle i det til sin ødeleggelse!
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 Da skal min sjel glede sig i Herren, fryde sig i hans frelse;
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 alle mine ben skal si: Herre, hvem er som du, du som frir den elendige fra den som er ham for sterk, og den elendige og fattige fra den som plyndrer ham?
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 Der opstår urettferdige vidner, de spør mig om det jeg ikke vet.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 De gjengjelder mig godt med ondt; min sjel er forlatt.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 Og jeg, jeg klædde mig i sørgeklær, da de var syke; jeg plaget min sjel med faste, og min bønn vendte tilbake til min barm.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 Jeg gikk omkring, som om det var min venn, min bror; jeg gikk nedbøiet i sørgeklær som en som sørger over sin mor.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 Men nu da jeg vakler, gleder de sig og flokker sig sammen; skarns-folk flokker sig om mig uten at jeg visste det; de sønderriver og hviler ikke.
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 Som skamløse som spotter for et stykke brød, skjærer de tenner imot mig.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Herre, hvor lenge vil du se til? Fri min sjel ut fra deres ødeleggelser, mitt eneste fra de unge løver.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 Jeg vil prise dig i en stor forsamling, love dig blandt meget folk.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 La ikke dem glede sig over mig, som uten grunn er mine fiender! La ikke dem som hater mig uten årsak, blinke med øiet!
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 For de taler ikke fred, men optenker svik mot de stille i landet.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 Og de lukker sin munn vidt op imot mig, de sier: Ha, ha! Der ser vårt øie!
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Du ser det, Herre, ti ikke! Herre, vær ikke langt borte fra mig!
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Våkn op og bli våken for å gi mig rett, min Gud og Herre, for å føre min sak!
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Døm mig efter din rettferdighet, Herre min Gud, og la dem ikke glede sig over mig!
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 La dem ikke si i sitt hjerte: Ha! Efter ønske! La dem ikke si: Vi har opslukt ham!
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 La alle dem få skam og bli til skamme som gleder sig ved min ulykke! La dem som ophøier sig over mig, klæs i skam og skjensel!
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 La dem juble og glede sig som unner mig min rett, og la dem alltid si: Høilovet være Herren, som unner sin tjener at det går ham vel!
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 Da skal min tunge synge om din rettferdighet, hele dagen om din pris.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.

< Salmenes 35 >