< Salmenes 33 >
1 Juble, I rettferdige, i Herren! For de opriktige sømmer sig lovsang.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Pris Herren med citar, lovsyng ham til tistrenget harpe!
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Syng en ny sang for ham, spill liflig med frydesang!
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 For Herrens ord er sant, og all hans gjerning er trofast.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 Han elsker rettferdighet og rett; jorden er full av Herrens miskunnhet.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 Himlene er skapt ved Herrens ord, og all deres hær ved hans munns ånde.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 Han samler havets vann som en dynge, han legger de dype vann i forrådshus.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 All jorden frykte for Herren, for ham beve alle de som bor på jorderike!
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 For han talte, og det skjedde; han bød, og det stod der.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 Herren omstøter hedningenes råd, han gjør folkenes tanker til intet.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 Herrens råd står fast evindelig, hans hjertes tanker fra slekt til slekt.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Salig er det folk hvis Gud Herren er, det folk han har utvalgt til sin arv.
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 Fra himmelen skuer Herren ned han ser alle menneskenes barn.
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 Fra det sted hvor han bor, ser han ned til alle dem som bor på jorden,
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 han som har skapt deres hjerter alle sammen, han som gir akt på alle deres gjerninger.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 En konge frelses ikke ved sin store makt, en helt reddes ikke ved sin store kraft.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 Hesten er ikke å stole på til frelse, og med sin store styrke redder den ikke.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Se, Herrens øie ser til dem som frykter ham, som bier på hans miskunnhet,
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 for å utfri deres sjel fra døden og holde dem i live i hungersnød.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Vår sjel bier på Herren; han er vår hjelp og vårt skjold.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 For i ham fryder vårt hjerte sig, fordi vi setter vår lit til hans hellige navn.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Din miskunnhet, Herre, være over oss, således som vi håper på dig!
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.