< Salmenes 18 >
1 Til sangmesteren; av Herrens tjener David, som talte denne sangs ord til Herren den dag da Herren hadde utfridd ham av alle hans fienders hånd og av Sauls hånd. Og han sa: Herre, jeg har dig hjertelig kjær, min styrke!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 Herren er min klippe og min festning og min frelser; min Gud er min klippe, som jeg setter min lit til, mitt skjold og min frelses horn, min borg.
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 Jeg påkaller den Høilovede, Herren, og blir frelst fra mine fiender.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 Dødens rep omspente mig, og fordervelsens strømmer forferdet mig.
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 Dødsrikets rep omgav mig, dødens snarer overfalt mig. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
6 I min trengsel påkalte jeg Herren, og jeg ropte til min Gud; han hørte fra sitt tempel min røst, og mitt skrik kom for ham, til hans ører.
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Da rystet og bevet jorden, og fjellenes grunnvoller skalv, og de rystet, for hans vrede var optendt.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 Det steg røk op av hans nese, og fortærende ild fra hans munn; glør brente ut av ham.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 Og han bøide himmelen og steg ned, og det var mørke under hans føtter.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 Og han fór på kjeruber og fløi, og han fór hastig frem på vindens vinger.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 Han gjorde mørke til sitt dekke, rundt omkring sig til sitt skjul, mørke vann, tykke skyer.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 Frem av glansen foran ham fór hans skyer frem, hagl og gloende kull.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 Og Herren tordnet i himmelen, den Høieste lot sin røst høre, hagl og gloende kull.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 Og han utsendte sine piler og spredte dem omkring - lyn i mengde og forvirret dem.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Da kom vannenes strømmer til syne, og jordens grunnvoller blev avdekket ved din trusel, Herre, for din neses åndepust.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 Han rakte sin hånd ut fra det høie, han grep mig; han drog mig op av store vann.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 Han fridde mig ut fra min sterke fiende og fra mine avindsmenn; for de var mig for mektige.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 De overfalt mig på min motgangs dag; men Herren blev min støtte.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 Og han førte mig ut i fritt rum; han frelste mig, for han hadde behag i mig.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 Herren gjengjeldte mig efter min rettferdighet, han betalte mig efter mine henders renhet.
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 For jeg tok vare på Herrens veier og vek ikke i ondskap fra min Gud.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 For alle hans lover hadde jeg for øie, og hans bud lot jeg ikke vike fra mig.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 Og jeg var ulastelig for ham og voktet mig vel for min synd.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 Og Herren gjengjeldte mig efter min rettferdighet, efter mine henders renhet for hans øine.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 Mot den fromme viser du dig from, mot den rettvise mann viser du dig rettvis,
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 mot den rene viser du dig ren, mot den forvendte viser du dig vrang.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 For du frelser elendige folk, og du fornedrer høie øine.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 For du lar min lampe skinne; Herren min Gud opklarer mitt mørke.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 For ved dig stormer jeg løs på fiendeskarer, og ved min Gud springer jeg over murer.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 Gud, hans vei er fullkommen; Herrens ord er rent, han er et skjold for alle dem som setter sin lit til ham.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 For hvem er Gud foruten Herren, og hvem er en klippe, uten vår Gud?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 Den Gud som omgjorder mig med kraft og gjør min vei fri for støt,
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 som gir mig føtter likesom hindene og stiller mig på mine høider,
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 som oplærer mine hender til krig, så mine armer spenner kobberbuen.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Og du gir mig din frelse til skjold, og din høire hånd støtter mig, og din mildhet gjør mig stor.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 Du gjør rummet vidt for mine skritt under mig, og mine ankler vakler ikke.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 Jeg forfølger mine fiender og når dem, og jeg vender ikke tilbake før jeg har gjort ende på dem.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 Jeg knuser dem, så de ikke makter å reise sig; de faller under mine føtter.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Og du omgjorder mig med kraft til krig, du bøier mine motstandere under mig.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 Og mine fiender lar du vende mig ryggen, og mine avindsmenn utrydder jeg.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 De roper, men der er ingen frelser - til Herren, men han svarer dem ikke.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 Og jeg knuser dem som støv for vinden, jeg tømmer dem ut som søle på gatene.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 Du redder mig fra folkekamper, du setter mig til hode for hedninger; folkeferd som jeg ikke kjenmer, tjener mig.
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 Bare de hører om mig, blir de mig lydige; fremmede kryper for mig.
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Fremmede visner bort og går bevende ut av sine borger.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 Herren lever, og priset er min klippe, og ophøiet er min frelses Gud,
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 den Gud som gir mig hevn og legger folkeferd under mig,
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 som frir mig ut fra mine fiender; ja, over mine motstandere ophøier du mig, fra voldsmannen redder du mig.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 Derfor vil jeg prise dig iblandt hedningene, Herre, og lovsynge ditt navn.
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 Han gjør frelsen stor for sin konge, han gjør miskunnhet mot sin salvede, mot David og mot hans ætt til evig tid.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.