< Salmenes 137 >

1 Ved Babylons elver, der satt vi og gråt når vi kom Sion i hu.
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 På vidjene der hengte vi våre harper;
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 for der krevde våre fangevoktere sanger av oss, våre plagere at vi skulde være glade: Syng for oss av Sions sanger!
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 Hvorledes skulde vi synge Herrens sang på fremmed jord?
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 Glemmer jeg dig, Jerusalem, da glemme mig min høire hånd!
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 Min tunge henge fast ved min gane om jeg ikke kommer dig i hu, om jeg ikke setter Jerusalem over min høieste glede!
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Kom Jerusalems dag i hu, Herre, så du straffer Edoms barn, dem som sa: Riv ned, riv ned, like til grunnen i den!
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 Babels datter, du ødelagte! Lykksalig er den som gir dig gjengjeld for den gjerning du gjorde mot oss.
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Lykksalig er den som griper og knuser dine spede barn imot klippen.
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Salmenes 137 >