< Salmenes 132 >

1 En sang ved festreisene. Herre, gi David lønn for hans møie,
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 han som tilsvor Herren, gav Jakobs Veldige det løfte:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 Jeg vil ikke gå inn i mitt huses telt, jeg vil ikke stige op på min sengs leie,
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 jeg vil ikke unne mine øine søvn, mine øielokk slummer,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 før jeg finner et sted for Herren, en bolig for Jakobs Veldige!
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Se, vi hørte om den i Efrata, vi fant den i skogsbygden.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Vi vil komme til hans bolig, vi vil tilbede for hans føtters skammel.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Reis dig, Herre, og kom til ditt hvilested, du og din styrkes ark!
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 La dine prester klæ sig i rettferd og dine fromme rope med fryd!
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 For Davids, din tjeners skyld vise du ikke din salvedes åsyn tilbake!
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 Herren har svoret David en sann ed, som han ikke vil gå fra: Av ditt livs frukt vil jeg sette konger på din trone;
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 dersom dine barn holder min pakt og mine vidnesbyrd, som jeg vil lære dem, da skal også deres barn for all tid sitte på dine trone.
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 For Herren har utkåret Sion, han har attrådd det til sin bolig:
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 Dette er mitt hvilested til evig tid; her vil jeg bo, fordi jeg har attrådd det.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Dets mat vil jeg velsigne, dets fattige vil jeg mette med brød,
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 og dets prester vil jeg klæ med fryd.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Der vil jeg la et horn vokse op for David, gjøre i stand en lampe for min salvede.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Hans fiender vil jeg klæ i skam, men på ham skal hans krone stråle.
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”

< Salmenes 132 >