< Salmenes 126 >
1 En sang ved festreisene. Da Herren lot Sions fanger vende tilbake, var vi som drømmende;
Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
2 da fyltes vår munn med latter, og vår tunge med jubel, da sa de iblandt hedningene: Store ting har Herren gjort imot disse.
Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
3 Store ting har Herren gjort imot oss; vi blev glade.
Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
4 Herre, la våre fanger vende tilbake likesom bekker i sydlandet!
Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
5 De som sår med gråt, skal høste fryderop.
Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
6 De går gråtende og bærer den de strør ut; de kommer hjem fryderop og bærer sine kornbånd.
Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.