< Salmenes 112 >

1 Halleluja! Salig er den mann som frykter Herren, som har sin store lyst i hans bud.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 Hans avkom skal være mektig på jorden; de opriktiges slekt skal velsignes.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Det er velstand og rikdom i hans hus, og hans rettferdighet står fast evindelig.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 Det går op et lys i mørket for de opriktige, for den som er nådig og barmhjertig og rettferdig.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 Lykkelig er den mann som forbarmer sig og låner ut; han hevder all sin sak i dommen.
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 For han skal ikke rokkes evindelig; den rettferdige skal være i evig minne.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 Han skal ikke frykte for nogen ond tidende; hans hjerte er fast, det setter sin lit til Herren.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 Hans hjerte er trygt; han frykter ikke, inntil han ser med lyst på sine fiender.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 Han har strødd ut, han har gitt de fattige; hans rettferdighet står fast evindelig, hans horn skal ophøies med ære.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 Den ugudelige skal se det og harmes, han skal skjære tenner og optæres; de ugudeliges attrå blir til intet.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Salmenes 112 >