< Salomos Ordsprog 30 >

1 Agurs, Jakes sønns ord og utsagn. Så talte mannen til Itiel, til Itiel og Ukkal:
Maganganun Agur ɗan Yake, magana ce horarriya. Wannan mutum ya furta wa Itiyel da kuma ga Ukal,
2 Jeg er for ufornuftig til å kalles menneske; manns forstand har jeg ikke.
“Ni ne mafi jahilci a cikin mutane; ba ni da fahimi irin na mutum.
3 Jeg har ikke lært visdom og har ikke kunnskap om den Hellige.
Ban koyi hikima ba, ba ni kuma da sani game da Mai Tsarkin nan,
4 Hvem fór op til himmelen og fór ned? Hvem samlet været i sine never? Hvem bandt vannet i et klæde? Hvem satte alle jordens grenser? Hvad er hans navn, og hvad er hans sønns navn? Du vet det jo.
Wane ne ya taɓa haura zuwa sama ya dawo? Wane ne ya tattara iska a tafin hannuwansa? Wane ne ya nannaɗe ruwaye a cikin rigarsa? Wane ne ya kafa dukan iyakokin duniya? Mene ne sunansa, da kuma sunan ɗansa? Faɗa mini in ka sani!
5 Alt Guds ord er rent; han er et skjold for dem som tar sin tilflukt til ham.
“Kowace maganar Allah ba ta da kuskure; shi ne garkuwa ga waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.
6 Legg ikke noget til hans ord, forat han ikke skal straffe dig, og du stå som en løgner!
Kada ka ƙara ga maganarsa, in ba haka ba zai tsawata maka ya kuma nuna kai maƙaryaci ne.
7 To ting beder jeg dig om, nekt mig dem ikke, før jeg dør:
“Abu biyu ina roƙonka, ya Ubangiji; kada ka hana ni kafin in mutu.
8 La falskhet og løgnens ord være langt borte fra mig! Gi mig ikke armod og heller ikke rikdom! La mig ete mitt tilmålte brød,
Ka kawar da ƙarya da kuma ƙarairayi nesa da ni; kada ka ba ni talauci ko arziki, amma ka ba ni abincina na yini kaɗai.
9 forat jeg ikke når jeg blir mett, skal fornekte dig og si: Hvem er Herren? og ikke når jeg blir fattig, stjele og forbanne min Guds navn!
In ba haka ba, zan wadace in ƙi ka har in ce, ‘Wane ne Ubangiji?’ Ko kuwa in zama matalauci in yi sata ta haka in kunyata sunan Allahna.
10 Baktal ikke en tjener for hans herre, forat han ikke skal banne dig, og du dra skyld over dig!
“Kada ka baza ƙarairayi game da bawa ga maigidansa, in ba haka ba, zai la’ance ka, za ka kuwa sha wahala a kan haka.
11 Der er en ætt som banner sin far og ikke velsigner sin mor,
“Akwai waɗanda sukan zagi mahaifinsu ba sa kuma sa wa mahaifiyarsu albarka;
12 en ætt som er ren i sine egne øine og dog ikke har tvettet sig for sitt eget skarn,
waɗanda sukan ɗauka su tsarkaka ne a ganinsu alhali kuwa ƙazamai ne su;
13 en ætt - hvor stolte er ikke dens øine, og dens øielokk, hvor hever de sig ikke! -
waɗanda kullum idanunsu masu kallon reni ne, waɗanda kallon da suke yi na daurin gira ne;
14 en ætt hvis tenner er sverd, og hvis jeksler er kniver, som eter arminger ut av landet og fattige ut av menneskenes tall.
waɗanda haƙoransu takuba ne waɗanda kuma muƙamuƙansu tarin wuƙaƙe ne don su cinye matalauta daga duniya da kuma mabukata daga cikin mutane.
15 Blodiglen har to døtre: Gi hit! Gi hit! Der er tre som aldri blir mette, fire som aldri sier: Nok!
“Matsattsaku tana da’ya’ya mata biyu. Suna kuka suna cewa, ‘Ba ni! Ba ni!’ “Akwai abubuwa uku da ba sa taɓa ƙoshi, guda huɗu ba sa taɓa cewa, ‘Ya isa!’
16 Det er dødsriket og det ufruktbare morsliv, jorden, som aldri blir mett av vann, og ilden, som aldri sier: Nok! (Sheol h7585)
Kabari, mahaifar da ba ta haihuwa, ƙasa, wadda ba ta taɓa ƙoshi da ruwa, da kuma wuta, wadda ba ta taɓa cewa ‘Ya isa!’ (Sheol h7585)
17 Et øie som spotter far og forakter lydighet mot mor, det skal ravnene ved bekken hakke ut, og ørneunger skal ete det.
“Idon da yake yi wa mahaifi ba’a, wanda yake wa mahaifiya dariyar rashin biyayya, hankakin kwari za su ƙwaƙule masa ido, ungulai za su cinye su.
18 Det er tre ting som er mig for underlige, og fire som jeg ikke skjønner:
“Akwai abubuwa uku da suke ba ni mamaki, abubuwa huɗu da ba na iya fahimtarsu,
19 Ørnens vei på himmelen, ormens vei over stenen, skibets vei på havet og en manns vei til en jomfru.
yadda gaggafa take firiya a sararin sama, yadda maciji yake tafiya a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, da kuma sha’ani tsakanin namiji da’ya mace.
20 Slik bærer en horkvinne sig at: Hun eter og tørker sin munn og sier: Jeg har ikke gjort noget ondt.
“Ga yadda mazinaciya take yi. Takan ci ta share bakinta ta ce, ‘Ban yi wani abu marar kyau ba.’
21 Under tre skjelver jorden, og under fire kan den ikke holde ut:
“Akwai abubuwa uku da duniya kan yi rawan jiki, abubuwa huɗu da ba ta iya jurewa,
22 under en træl når han blir konge, og en dåre når han blir mett av brød,
bawan da ya zama sarki, wawan da ya ƙoshi da abinci,
23 under en forsmådd kvinne når hun blir gift, og en tjenestepike når hun arver sin frue.
macen da ba a ƙauna wadda ta sami miji, da kuma baiwar da ta ɗauki matsayin uwargijiyarta.
24 Det er fire som er små på jorden og allikevel overvettes vise:
“Akwai abubuwa huɗu a duniya da suke ƙanana, duk da haka suna da hikima ƙwarai.
25 Maurene er ikke noget sterkt folk, og enda lager de sin føde om sommeren;
Kyashi halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka suna ajiyar abincinsu da rani;
26 fjellgrevlingene er ikke noget kraftig folk, og enda bygger de sitt hus i berget;
remaye halittu ne da ba su da ƙarfi sosai, duk da haka sukan yi gidajensu a duwatsu;
27 gresshoppene har ingen konge, og enda drar de alle ut, skare efter skare;
fāra ba su da sarki, duk da haka suna tafiya tare bisa ga girma;
28 firfislen kan du gripe med hendene, og allikevel finnes den i kongelige palasser.
ana iya kama ƙadangare da hannu, duk da haka akan same shi a fadodin sarakuna.
29 Det er tre som skrider vakkert frem, og fire som har en vakker gang:
“Akwai abubuwa uku da suke jan jiki da kuma taƙama a tafiyarsu abubuwa huɗu waɗanda suke kwarjini da taƙama a tafiyarsu,
30 Løven, som er en helt blandt dyrene, og som ikke vender om for nogen,
zaki mai ƙarfi a cikin namun jeji, wanda ba ya ratse wa kowa;
31 hesten med gjord om lendene, bukken, og en konge i spissen for sitt folk.
zakara mai taƙama, da bunsuru, da kuma sarki mai sojoji kewaye da shi.
32 Har du vært så uforstandig at du har ophøiet dig, eller har du tenkt på ondt, da legg hånden på din munn!
“In ka yi wauta ka kuma ɗaukaka kanka, ko kuwa wani yana ƙulla maka mugunta, ka dāfa hannunka a bisa bakinka!
33 For trykk på melk gir smør, og trykk på nese gir blod, og trykk på vrede gir trette.
Gama kamar yadda kaɗaɗɗen madara takan kawo mai, murɗa hanci kuma takan sa a yi haɓo, haka tsokanar fushi takan kawo faɗa.”

< Salomos Ordsprog 30 >