< Nehemias 3 >

1 Ypperstepresten Eljasib og hans brødre og prestene gjorde sig rede og bygget Fåreporten; de helliget den og satte inn dørene; så bygget de videre til Mea-tårnet, som de helliget, og videre frem til Hananel-tårnet.
Eliyashib babban firist da’yan’uwansa firistoci suka tashi suka sāke gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa ƙofofinta a wurarensu, suka yi ginin har Hasumiyar Ɗari, wadda suka tsarkake, da kuma Hasumiyar Hananel.
2 Ved siden av dem bygget mennene fra Jeriko og ved siden av dem Sakkur, Imris sønn.
Mutanen Yeriko kuwa suka kama ginin daga mahaɗin, Zakkur ɗan Imri kuma ya fara ginin biye da su.
3 Fiskeporten blev bygget av Sena'as barn; de tømret den op og satte inn dører, låser og slåer.
’Ya’yan Hassenaya ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka kafa ginshiƙan, suka kuma sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu.
4 Ved siden av dem arbeidet Meremot, sønn av Uria, Hakkos' sønn, ved siden av ham Mesullam, sønn av Berekja, Mesesabels sønn, og ved siden av ham Sadok, Ba'anas sønn.
Kusa da su kuma, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz ne ya yi gyare-gyaren. Biye da shi kuma sai Meshullam ɗan Berekiya, ɗan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi Zadok ɗan Ba’ana shi ma ya yi gyare-gyare.
5 Ved siden av ham arbeidet folkene fra Tekoa; men de fornemme blandt dem bøide ikke sin nakke under arbeidet for sin Herre.
Mutanen Tekowa ne suka yi gyare-gyare biye da shi, amma manyan garinsu suka ƙi su sa hannu cikin aikin da shugabanninsu suka bayar.
6 Den gamle port blev satt i stand av Jojada, Paseahs sønn, og Mesullam, Besodjas sønn; de tømret den op og satte inn dører og låser og slåer.
Yohiyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodehiya ne suka gyara Ƙofar Yeshana. Suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.
7 Ved siden av dem arbeidet gibeonitten Melatja og meronotitten Jadon med mennene fra Gibeon og Mispa, som hørte under stattholderens domstol hinsides elven.
Biye da su, mutanen Gibeyon da Mizfa Melatiya na Gibeyon da Yadon Meronot waɗanda suke ƙarƙashin ikon gwamnan Kewayen Kogin Yuferites ne suka yi gyare-gyaren.
8 Ved siden av dem arbeidet Ussiel, Harhajas sønn, en gullsmed, og ved siden av ham Hananja, en av salvelagerne. Det næste stykke av Jerusalems mur lot de være like til den brede mur.
Uzziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin masu ƙeran zinariya ne ya yi gyare-gyaren sashe na biye; sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyaren biye da wannan. Suka gyara Urushalima har zuwa Katanga Mai Faɗi.
9 Ved siden av dem arbeidet Refaja, Hurs sønn, høvdingen over den ene halvdel av Jerusalems distrikt.
Refahiya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyaren sashe na biye.
10 Ved siden av ham arbeidet Jedaja, Harumafs sønn, midt imot sitt eget hus, og ved siden av ham Hattus, Hasabnejas sønn.
Kusa da Refahiya, Yedahiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyaren daga gaban gidansa, sai Hattush ɗan Hashabnehiya ya yi gyare-gyaren biye da shi.
11 Et annet stykke blev satt i stand av Malkia, Harims sønn, og Hassub, Pahat-Moabs sønn, og dessuten Ovnstårnet.
Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-Mowab ya yi gyare-gyaren wani sashe da kuma Hasumiyar Wurin Gashi.
12 Ved siden av ham arbeidet Sallum, sønn av Hallohes, høvdingen over den andre halvdel av Jerusalems distrikt, og sammen med ham hans døtre.
Shallum ɗan Hallohesh, mai mulkin ɗayan rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyaren sashe na biye tare da taimakon’ya’yansa mata.
13 Dalporten blev satt i stand av Hanun og innbyggerne i Sanoah; de bygget den og satte inn dører, låser og slåer; de bygget også tusen alen av muren, til Møkkporten.
Hanun da mazaunan Zanowa ne suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sāke gina ta suka sa ƙofofinta, da sakatunta, da sandunan ƙarfenta a wurarensu. Suka kuma gyara yadi ɗari biyar na katangar har zuwa Ƙofar Juji.
14 Og Møkkporten blev satt i stand av Malkia, Rekabs sønn, høvdingen over Bet-Hakkerems distrikt; han bygget den op og satte inn dører og låser og slåer.
Malkiya ɗan Rekab mai mulkin yankin Bet-Hakkerem ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Juji. Ya sāke gina ta ya kuma sa sakatunta, da sanduna ƙarfenta a wurarensu.
15 Kildeporten blev satt i stand av Sallun, Kol-Hoses sønn, høvdingen over Mispas distrikt; han bygget den, la tak på den og satte inn dører, låser og slåer; likeledes bygget han muren ved Selah-dammen ved kongens have helt frem til de trapper som går ned fra Davids stad.
Shallum ɗan Kol-Hoze mai mulkin Mizfa ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Maɓuɓɓuga. Ya sāke gina ta, ya yi mata jinƙa yana sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu. Ya kuma gyara katangar tafkin Silowam, ta Lambun Sarki, har zuwa matakalan da suka gangara daga Birnin Dawuda.
16 Efter ham arbeidet Nehemias, Asbuks sønn, høvdingen over den ene halvdel av Betsurs distrikt, til midt imot Davids graver og til den gravde dam og til heltenes hus.
Gaba da shi, Nehemiya ɗan Azbuk, mai mulkin rabin yankin Bet-Zur ne ya yi gyare-gyaren har zuwa kusa da kaburburan Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da kuma Gidan Jarumawa.
17 Efter ham arbeidet levittene under Rehum, Banis sønn; ved siden av ham arbeidet Hasabja, høvdingen over den ene halvdel av Ke'ilas distrikt, for sitt distrikt.
Biye da shi, Lawiyawa a ƙarƙashin Rehum ɗan Bani ne suka yi gyare-gyaren. Kusa da su, Hashabiya mai mulkin rabin yankin Keyila ne ya yi gyare-gyaren don yankinsa.
18 Efter ham arbeidet deres brødre under Bavvai, Henadads sønn, høvdingen over den andre halvdel av Ke'ilas distrikt.
Biye da shi,’yan’uwansu Lawiyawa ne a ƙarƙashin Binnuyi ɗan Henadad, mai mulkin ɗayan rabin yankin Keyila suka yi gyare-gyaren.
19 Ved siden av ham arbeidet Eser, Josvas sønn, høvdingen over Mispa, på et annet stykke, fra plassen midt imot opgangen til våbenhuset i Vinkelen.
Biye da su, Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya yi gyara wani sashe, daga inda yake fuskantar hawan gidan makamai har zuwa kusurwa.
20 Efter ham arbeidet Baruk, Sabbais sønn, med stor iver på et annet stykke, fra Vinkelen og til døren på ypperstepresten Eljasibs hus.
Biye da shi, Baruk ɗan Zakkai da ƙwazo ya gyara wani sashe, daga kusurwa zuwa mashigin gidan Eliyashib babban firist.
21 Efter ham arbeidet Meremot, sønn av Uria, Hakkos' sønn, på et annet stykke, fra døren på Eljasibs hus og til enden av hans hus.
Biye da shi, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya yi gyaran wani sashe, daga mashigin gidan Eliyashib zuwa ƙarshensa.
22 Efter ham arbeidet prestene, mennene fra Jordan-sletten.
Firistoci daga kewayen yankin ne suka yi gyare-gyaren biye da shi.
23 Efter dem arbeidet Benjamin og Hasub midt imot sitt eget hus; efter dem arbeidet Asarja, sønn av Ma'aseja, Ananjas sønn, ved siden av sitt hus.
Can gaba da su, Benyamin da Hasshub ne suka yi gyare-gyaren a gaban gidansu, biye da su kuwa, Azariya ɗan Ma’asehiya, ɗan Ananiya ne ya yi gyare-gyaren kusa da gidansa.
24 Efter ham arbeidet Binnui, Henadads sønn, på et annet stykke, fra Asarjas hus til Vinkelen og til det sted hvor muren bøier av.
Biye da shi, Binnuyi ɗan Henadad ya yi gyaran wani sashe, daga gidan Azariya zuwa kusurwa,
25 Palal, Usais sønn, arbeidet fra stedet midt imot Vinkelen og det tårn som springer frem fra kongens øvre hus ved fengselsgården; efter ham arbeidet Pedaja, Paros' sønn.
sai Falal ɗan Uzai ya yi aiki ɗaura da kusurwa da kuma doguwar hasumiya daga fadar da take bisa kusa da shirayin masu tsaro. Biye da shi, Fedahiya ɗan Farosh
26 - Tempeltjenerne bodde på Ofel, til plassen midt imot Vannporten mot øst og det fremspringende tårn -.
da masu hidimar haikali da suke zama a tudun Ofel ne suka yi gyare-gyaren har zuwa wani wuri ɗaura da Ƙofar Ruwa wajen gabas da kuma doguwar hasumiya.
27 Efter ham arbeidet folkene fra Tekoa på et annet stykke, fra plassen midt imot det store fremspringende tårn og til Ofel-muren.
Biye da su, mutanen Tekowa suka yi gyaran wani sashe, daga babbar doguwar hasumiya zuwa katangar Ofel.
28 Ovenfor Hesteporten arbeidet prestene, hver av dem midt imot sitt eget hus.
Daga Ƙofar Doki, firistoci ne suka yi gyare-gyaren, kowanne a gaban gidansa.
29 Efter dem arbeidet Sadok, Immers sønn, midt imot sitt eget hus, og efter ham Semaja, Sekanjas sønn, som hadde vaktholdet ved den østre port.
Biye da su, Zadok ɗan Immer ya yi gyare-gyaren ɗaura da gidansa. Biye da shi, Shemahiya ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.
30 Efter ham arbeidet Hananja, Selemjas sønn, og Hanun, Salafs sjette sønn, på et annet stykke, og efter dem Mesullam, Berekjas sønn, midt imot sitt kammer.
Biye da shi, Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashe. Biye da su, Meshullam ɗan Berekiya ya yi gyare-gyaren ɗaura da wurin zamansa.
31 Efter ham arbeidet Malkia, en av gullsmedene, frem til tempeltjenernes og kremmernes hus, midt imot Mønstringsporten og frem til Hjørnesalen.
Biye da shi, Malkiya, ɗaya daga cikin masu ƙera zinariya ya yi gyare-gyaren har zuwa gidan masu hidimar haikali da kuma’yan kasuwa, ɗaura da Ƙofar Bincike, har zuwa ɗakin da yake bisa kusurwar.
32 Og mellem Hjørnesalen og Fåreporten arbeidet gullsmedene og kremmerne.
Maƙeran zinariya da’yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin ɗakin da yake bisa kusurwa da Ƙofar Tumaki.

< Nehemias 3 >