< Nehemias 12 >

1 Dette er de prester og levitter som drog hjem med Serubabel, Sealtiels sønn, og Josva: Seraja, Jirmeja, Esras,
Waɗannan su ne firistoci da Lawiyawa waɗanda suka komo tare da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da kuma Yeshuwa. Serahiya, Irmiya, Ezra,
2 Amarja, Malluk, Hattus,
Amariya, Malluk, Hattush
3 Sekanja, Rehum, Meremot,
Shekaniya, Rehum, Meremot,
4 Iddo, Ginnetoi, Abia,
Iddo, Ginneton, Abiya,
5 Mijamin, Ma'adja, Bilga,
Miyamin, Mowadiya, Bilga,
6 Semaja, Jojarib, Jedaja,
Shemahiya, Yohiyarib, Yedahiya,
7 Sallu, Amok, Hilkia og Jedaja. Disse var overhodene for prestene og for sine brødre på Josvas tid.
Sallu, Amok, Hilkiya da Yedahiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da’yan’uwansu a kwanakin Yeshuwa.
8 Og levittene var: Josva, Binnui, Kadmiel, Serebja, Juda og Mattanja, som sammen med sine brødre forestod lovsangen,
Lawiyawan su ne Yeshuwa, Binnuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da kuma Mattaniya, wanda tare da’yan’uwansa yake lura da waƙoƙin godiya.
9 mens deres brødre Bakbukja og Unno stod midt imot dem for å vareta sin tjeneste.
Bakbukiya da Unni,’yan’uwansu sun tsaya ɗaura da su a hidimomi.
10 Josva fikk sønnen Jojakim, Jojakim fikk Eljasib, Eljasib fikk Jojada,
Yeshuwa ne mahaifin Yohiyakim, Yohiyakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib shi ne mahaifin Yohiyada,
11 Jojada fikk Jonatan, og Jonatan fikk Jaddua.
Yohiyada shi ne mahaifin Yonatan, Yonatan kuma mahaifin Yadduwa.
12 På Jojakims tid var disse prestenes familie-overhoder: for Serajas familie Meraja, for Jirmejas Hananja,
A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
13 for Esras' Mesullam, for Amarjas Johanan,
na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
14 for Melukis Jonatan, for Sebanjas Josef,
na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
15 for Harims Adna, for Merajots Helkai,
na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
16 for Iddos Sakarias, for Ginnetons Mesullam,
na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
17 for Abias Sikri, for Minjamins, for Moadjas Piltai,
na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
18 for Bilgas Sammua, for Semajas Jonatan,
na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
19 for Jojaribs Mattenai, for Jedajas Ussi,
na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
20 for Sallais Kallai, for Amoks Eber,
na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
21 for Hilkias Hasabja og for Jedajas Netanel.
na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
22 I Eljasibs, Jojadas, Johanans og Jadduas tid blev levittenes familieoverhoder optegnet, likeså prestene under perseren Darius' regjering.
Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
23 Familie-overhodene for Levis barn blev optegnet i krønikeboken, og det like til Johanans, Eljasibs sønns tid.
Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
24 Levittenes overhoder var: Hasabja, Serebia og Josva, Kadmiels sønn, og deres brødre stod midt imot dem for å love og prise Gud, således som den Guds mann David hadde befalt, flokk ved flokk.
Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
25 Mattanja, Bakbukja, Obadja, Mesullam, Talmon og Akkub holdt som dørvoktere vakt over forrådskammerne ved portene.
Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
26 Disse levde i Jojakims, Josvas sønns, Josadaks sønns tid, og i stattholderen Nehemias' og i presten Esras', den skriftlærdes, tid.
Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
27 Til innvielsen av Jerusalems mur hentet de levittene fra alle deres bosteder og førte dem til Jerusalem for å holde innvielse og gledesfest både med lovprisning og med sang, med cymbler, harper og citarer.
A keɓewar katangar Urushalima, an nemi Lawiyawa daga inda suke zama aka kawo su Urushalima don su yi bikin miƙawa da farin ciki da waƙoƙin godiya da kuma kiɗin kuge, garaya da molo.
28 Og sangernes barn kom sammen både fra landet rundt om Jerusalem og fra netofatittenes landsbyer
Aka kuma tattara mawaƙa su ma daga yankin kewayen Urushalima, daga ƙauyukan Netofawa,
29 og fra Bet-Haggilgal og fra Gebas og Asmavets jorder; for sangerne hadde bygget sig landsbyer rundt omkring Jerusalem.
daga Bet-Gilgal, da kuma daga wuraren Geba da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.
30 Og prestene og levittene renset sig, og de renset folket og portene og muren.
Sa’ad da firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu da tsarki, sai suka tsarkake mutane, ƙofofi da kuma katanga.
31 Da lot jeg Judas høvdinger stige op på muren, og jeg opstilte to store lovsangskor og festtog; det ene gikk til høire ovenpå muren frem til Møkkporten;
Sai na sa shugabannin Yahuda suka haura zuwa bisan katangar. Na kuma sa manyan ƙungiyoyi biyu na mawaƙa su miƙa godiya. Ɗaya ya haura zuwa bisan katangar zuwa dama, wajen Ƙofar Juji.
32 og efter dem gikk Hosaja og halvdelen av Judas høvdinger,
Hoshahiya da rabin shugabannin Yahuda kuwa suka bi su,
33 Asarja, Esras og Mesullam,
tare da Azariya, Ezra, Meshullam,
34 Juda, Benjamin, Semaja og Jirmeja
Yahuda, Benyamin, Shemahiya, Irmiya,
35 og likeså nogen av prestenes barn, som bar trompeter; det var Sakarja, sønn av Jonatan, sønn av Semaja, sønn av Mattanja, sønn av Mikaja, sønn av Sakkur, sønn av Asaf,
da waɗansu firistoci kuma da ƙahoni, da kuma Zakariya ɗan Yonatan, ɗan Shemahiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mikahiya, ɗan Zakkur, ɗan Asaf,
36 og hans brødre Semaja og Asarel, Milalai, Gilalai, Ma'ai, Netanel, Juda og Hanani med den Guds mann Davids sanginstrumenter; og Esras, den skriftlærde, gikk foran dem.
da’yan’uwansa, Shemahiya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma’ai, Netanel, Yahuda da Hanani, tare da kayan kiɗi da Dawuda mutumin Allah ya umarta. Ezra malamin Doka ya jagoranci jerin gwanon.
37 De gikk over Kildeporten og rett frem, opover trappene til Davids stad, der hvor en stiger op på muren ovenfor Davids hus, helt frem til Vannporten i øst.
A Ƙofar Maɓuɓɓuga suka ci gaba kai tsaye suka haura matakalan Birnin Dawuda a kan hawa zuwa katangar suka wuce a bisa gidan Dawuda zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.
38 Det andre lovsangskor gikk til den motsatte side, og jeg fulgte efter det med den andre halvdel av folket, ovenpå muren, ovenfor Ovnstårnet, bort til den brede mur,
Ƙungiyar mawaƙa ta biyu suka yi jerin gwano a ɗaya gefen. Na bi su a bisan katangar, tare da rabin mutanen, muka wuce Hasumiya Tanderu zuwa Katanga Mai Faɗi,
39 og over Efra'im-porten, den gamle port og Fiskeporten, forbi Hananel-tårnet og Mea-tårnet, helt frem til Fåreporten; de stanset ved Fengselsporten.
bisa Ƙofar Efraim, Ƙofar Yeshana, Ƙofar Kifi, Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiya ɗari, har zuwa Ƙofar Tumaki. A Ƙofar Matsara suka tsaya.
40 Således stod begge lovsangskorene ved Guds hus, likeså jeg og halvdelen av formennene med mig
Ƙungiyoyin mawaƙa biyu da suka yi godiya suka ɗauki wurarensu a gidan Allah, haka ma ni, tare da rabin shugabanni,
41 og prestene Eljakim, Ma'aseja, Minjamin, Mikaja, Eljoenai, Sakarja og Hananja med trompeter,
da kuma firistoci, Eliyakim, Ma’asehiya, Miniyamin, Mikahiya, Eliyohenai, Zakariya da Hananiya tare da ƙahoninsu,
42 og Ma'aseja, Semaja, Eleasar, Ussi, Johanan, Malkia, Elam og Eser. Og sangerne istemte sangen, og den som ledet den, var Jisrahja.
haka ma Ma’asehiya, Shemahiya, Eleyazar, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam da Ezer. Mawaƙan suka rera waƙoƙi a ƙarƙashin kulawar Yezrahiya.
43 De ofret den dag store offer og gledet sig, for Gud hadde latt dem vederfares en stor glede; også kvinnene og barna gledet sig, og jubelen i Jerusalem hørtes lang vei.
A rana ta uku kuma suka miƙa manyan hadayu, suna farin ciki domin Allah ya ba su farin ciki mai girma. Mata da yara suka yi farin ciki su ma. An ji ƙarar farin ciki da ake yi a Urushalima daga nesa.
44 Samme dag blev det innsatt menn som skulde ha tilsyn med forrådskammerne for de hellige gaver, førstegrøden og tiendene; der skulde de samle fra bymarkene det som efter loven tilkom prestene og levittene; for det var glede i Juda over at prestene og levittene nu utførte sin tjeneste.
A lokacin an naɗa mutane su lura da ɗakunan ajiya don sadakoki, nunan fari da kuma zakka. Daga gonakin garuruwan da suke kewaye za su kawo sassan da Dokar ta umarta zuwa ɗakunan ajiya domin firistoci da Lawiyawa, gama Yahuda ya ji daɗin aikin firistoci da Lawiyawa.
45 Og de varetok hvad det var å vareta for deres Gud, og hvad det var å vareta ved renselsen; likeså varetok sangerne og dørvokterne sin tjeneste, således som David og hans sønn Salomo hadde befalt.
Sun yi hidimar Allahnsu da kuma hidimar tsarkakewa, kamar yadda mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, bisa ga umarnin Dawuda da ɗansa Solomon.
46 For allerede i gammel tid, i Davids og Asafs dager, var det ledere for sangerne, og det lød lov- og takkesanger til Gud.
Gama tun dā, a kwanakin Dawuda da Asaf, akwai masu bi da mawaƙa da kuma na waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.
47 Og i Serubabels og Nehemias' dager gav hele Israel sangerne og dørvokterne det som tilkom dem for hver dag; og de gav levittene hellige gaver, og levittene gav Arons barn hellige gaver.
Saboda haka a kwanakin Zerubbabel da Nehemiya, dukan Isra’ila suka ba da sashe na kowace rana domin mawaƙa da matsaran ƙofofi. Suka kuma keɓe sashe don sauran Lawiyawa, Lawiyawan kuma suka keɓe sashe don zuriyar Haruna.

< Nehemias 12 >